• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Goman Ƙarshe Na Watan Ramadan [Darajarsu Da Mutsayinsu] Na 1

by Nuhu Ubale Ibrahim
1 year ago
in Bakon Marubuci, Fatawa, Ilimi
0
Goman Ƙarshe Na Watan Ramadan [Darajarsu Da Mutsayinsu] Na 1
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Goman ƙarshen Ramadan su ne mafi girman dararen duniya baki ɗaya, domin a cikinsu Lailatul-Ƙadari yake. Allah Ta’ala Yana cewa: “Lailatul-Ƙadari ya fi wata dubu alheri” Suratul Ƙadri aya ta 3.

Babban malamin tafsiri al-Imam al-Bagawi, Allah Ya yi masa rahama yana cewa: “Malaman tafsiri sun bayyana ma’anar ayar da cewa: aikata aikin ƙwarai a cikin daren Lailatul-Ƙadari shi ne ya fi alheri sama da aikin ƙwarai a cikin watanni dubu wanda babu Lailatul-Ƙadari a cikinsu”

  • CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 1
  • SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1

Hadisi ya tabbata a cikin Al-mujtaba na Imam an-Nasa’i da Musnad na Imam Ahmad daga Abu Huraira Allah Ya ƙara yarda a gare shi ya ce: Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Ramadana ya zo muku, wata ne mai wata irin albrka, Allah Mai girma da ɗaukaka ya wajabta muku azumtar sa, ana buɗe ƙofofin Aljanna a cikinsa, ana kuma rufe ƙofofin Jahannama a cikinsa, a cikinsa akwai wani dare da ya fi wata dubu alheri, duk wanda aka haramta masa alherinsa, to, tabbas an haramta masa alheri”

Ya zo a cikin Sahihul Bukhari da Muslim, Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Duk wanda ya tsayu a daren Lailatul-Ƙadari yana mai imani da neman lada, to, an gafarta masa zunubansa”

Wannan dare yana cikin goman ƙarshe na Ramadan. Manzon Allah (S.A.W) ya kasance yana cewa da Sahabbai: Ku kirdadi Lailatul-Ƙadari a goman ƙarshe na Ramadan. Bukhari da Muslim ne suka ruwaito.

Labarai Masu Nasaba

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

Ana karɓo hadisi daga Nana Aishatu, Allah Ya ƙara yarda a gare ta, ta ce: Lalle Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Ku kirdadi Lailatul-Ƙadari a cikin dare mara na goman ƙarshe na Ramadana” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito.

Manzon Allah (S.AW) ya fi kowa girman matsayi da alfarma da daraja da martaba a wurin Allah. Allah Ya gafarta masa abin da ya aikata da wanda bai aikata ba amma duk da haka yana ƙara ƙaimi da ƙwazo a goman ƙarshe na Ramadan sama da ƙwazonsa a goman farko da ta tsakiya na wannan wata mai albarka. Nana Aisha Allah Ya ƙara mata yarda ta ce: “Manzon Allah (S.A.W) ya kasance idan goman ƙarshe ta shiga, sai ya ƙara zage dantse, ya kuma raya daren gaba ɗaya, kuma ya tayar da iyalansa daga barci” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito. A wata ruwaya ta Muslim cewa ta yi:” Manzon Allah (S.A.W) ya kasance yana ƙoƙari a goman ƙarshe irin ƙoƙarin da baya yinsa a waninsa”

Sayyadina Aliyu ɗan Abu Ɗalib, Allah Ya ƙara masa yarda ya ce: “Lalle annabi (S.A.W) ya kasance yana tayar da iyalansa a goman ƙarshe na Ramadana” Tirmizi ne ya ruwaito da salsala ingantacciya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 10 Karshe na RamadanAzumiLailatul KadriRamadan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Lokaci Ya Yi Da Kasashen Yamma Za Su Yi Watsi Da Tunanin Wai Sun Fi Sauran Kasashe

Next Post

Isra’ila Ta Kori Kafar Talabijin Ta Al Jazeera Daga Kasarta

Related

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari
Bakon Marubuci

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

2 hours ago
AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate
Ilimi

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

4 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

6 days ago
Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus
Bakon Marubuci

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

7 days ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

2 weeks ago
Next Post
Isra’ila Ta Kori Kafar Talabijin Ta Al Jazeera Daga Kasarta

Isra'ila Ta Kori Kafar Talabijin Ta Al Jazeera Daga Kasarta

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

July 11, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

July 11, 2025
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

July 11, 2025
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.