• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Guntun Gatarinka Ya Fi Sari Ka Ba Ni

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
gatari

Hausawa su kan ce, ”Guntun gatarinka ya fi sari ka ba ni.” Tunani na dogaro da kai da karfin zuci da wannan magana ta nuna, ba zai taba zama na tsohon yayi ba. 

 

A jihar Enugu ta kasar Najeriya, akwai wani nau’in abinci na gargajiya da ake kira Okpa, wanda ake yinsa da garin gujiya. A baya a kan kalli abincin a matsayin na matalauta, ganin yadda ake samunsa cikin sauki. Idan wani ya sha shayi da Okpa, maimakon abincin Turawa irinsu Biscuit da burodi, to, za a yi masa dariya. Sai dai daga bisani wani sarki mai suna Christian Onoh, ya daidaita yanayin da Okpa din ke ciki, inda ya gayyaci manyan mutane don su sha shayi da cin Okpa tare, har ma ya mai da Okpa a matsayin kyak din da ake ci yayin bikin ranar haihuwarsa.

  • NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars N2m, Ta Dakatar Da Ɗan Wasanta
  • Naim Qassem Ya Zama Sabon Shugaban Hezbollah

Bisa kokarinsa na yayata wannan abinci, sannu a hankali ya zama nau’in abinci mai farin jini a jihar Enugu da Najeriya baki daya. Sa’an nan binciken da masu nazarin kimiyya da fasaha suka yi, shi ma ya nuna cewa, Okpa din wani nau’in abinci ne mai gina jiki sosai.

 

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Wannan labari da aka bayyana shi cikin wata makalar da aka wallafa kan shafin yanar gizo na jaridar Punch ta kasar Najeriya ya nuna mana cewa, ya kamata a nuna karin imani, yayin da ake kula da wasu abubuwan gargajiya.

 

Hakika ci gaban zaman al’umma ya kan sa a kara darajantar abubuwa na gargajiya. A wannan fanni za mu iya duba misali na kasar Sin. A baya, lokacin da kasar ta zama karkashin hare-haren da wasu kasashe masu karfi suka kai mata, da fuskantar danniya a fannin tattalin arziki, da kutsa kai ta fuskar al’adu, Sinawa sun tantace al’adunta na gargajiya bisa kwatantawa da na kasashen yamma cikin zurfi, har ma sun yi la’akari da maye gurbin bakaken Sinanci da haruffan Turanci, don tabbatar da saukin rubutawa a lokacin. Sai dai a kasar Sin ta wannan zamani, mutanen kasar na kokarin kare wurare masu tarihi, da nazari a kansu, da gadon fasahohin al’adu. Yayin da matasa ke kallon tufafi, da kide-kide, da sauran alamu masu salon gargajiya a matsayin abubuwa masu farin jini. Kana duk wani birnin kasar na kokarin raya gidajen ajiyar kayayyakin tarihi, da tsoffin tituna da ungwanni, don nuna tarihi da al’adu na musamman da yake da su.

 

To amma ko mene ne ya sa ake darajantar al’adun gargajiya? Saboda asalin tunanin wata kasa yana cikin al’adunta na gargajiya. Dole ne a yi nazari kan al’adu da tunani na gargajiya, domin ta haka ne za a iya samun wata turbar raya kasa mai dacewa. Misali, manufar zamanantarwa ta kasar Sin ta kunshi bangaren samun jituwa tsakanin dan Adam da muhallin halittu, sai dai asalin bangaren shi ne tunanin Taoism na kasar, na ”duk wani abu da ni a hade suke.” Ban da haka, yadda tunanin zamanantarwa na kasar Sin ke dora muhimmanci kan tabbatar da wadatar daukacin al’umma, shi ma ya samu asalinsa ne daga tunanin gargajiyar kasar Sin na tabbatar da daidaituwa tsakanin al’umma.

 

Ban da haka, yadda ake kokarin kare al’adun gargajiya da raya shi, yana da amfani na musamman ga yunkurin warware matsalolin da duniyarmu ke fuskantar. Tun fil azal, Sinawa sun jaddada muhimmancin tsarin kasancewar duniya karkashin mallakar daukacin kasashe da al’ummun duniya. Saboda haka a ganin kasar, kamata ya yi, a samu daidaito da zumunta tsakanin mabambantan al’ummu. Wannan ra’ayi ya zama daya da tunanin Ubuntu dake yaduwa a nahiyar Afirka, wanda ya jaddada bukatar samun kauna, da huldar cude-ni-in-cude-ka tsakanin mutane.

 

A wannan zamanin da muke ciki, wadannan tunanin gargajiya na Sin da Afirka sun zama matsaya daya ta raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya, wanda ya tabbatar da yiwuwar kawo karshen rikici da nuna bambanci, da kare zaman lafiya da yanayin ci gaba a duniya.

 

A zahiri, ta hanyar dogaro da kai, da kokarin kare al’adun gargajiya, da cudanya tsakanin mabambantan al’adu, za a samar wa duniya da daukacin dan Adam karin abubuwa masu yakini, da tabbatar da makomarsu mai haske. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani
Ra'ayi Riga

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata
Ra'ayi Riga

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Next Post
Matatar dangote

Ba Za A Yi Layin Man Fetur Ba Idan 'Yan Kasuwa Suka Mayar Da Hankali Kan Matatarmu - Ɗangote 

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.