ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Guntun Gatarinka Ya Fi Sari Ka Ba Ni

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
gatari

Hausawa su kan ce, ”Guntun gatarinka ya fi sari ka ba ni.” Tunani na dogaro da kai da karfin zuci da wannan magana ta nuna, ba zai taba zama na tsohon yayi ba. 

 

A jihar Enugu ta kasar Najeriya, akwai wani nau’in abinci na gargajiya da ake kira Okpa, wanda ake yinsa da garin gujiya. A baya a kan kalli abincin a matsayin na matalauta, ganin yadda ake samunsa cikin sauki. Idan wani ya sha shayi da Okpa, maimakon abincin Turawa irinsu Biscuit da burodi, to, za a yi masa dariya. Sai dai daga bisani wani sarki mai suna Christian Onoh, ya daidaita yanayin da Okpa din ke ciki, inda ya gayyaci manyan mutane don su sha shayi da cin Okpa tare, har ma ya mai da Okpa a matsayin kyak din da ake ci yayin bikin ranar haihuwarsa.

ADVERTISEMENT
  • NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars N2m, Ta Dakatar Da Ɗan Wasanta
  • Naim Qassem Ya Zama Sabon Shugaban Hezbollah

Bisa kokarinsa na yayata wannan abinci, sannu a hankali ya zama nau’in abinci mai farin jini a jihar Enugu da Najeriya baki daya. Sa’an nan binciken da masu nazarin kimiyya da fasaha suka yi, shi ma ya nuna cewa, Okpa din wani nau’in abinci ne mai gina jiki sosai.

 

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Wannan labari da aka bayyana shi cikin wata makalar da aka wallafa kan shafin yanar gizo na jaridar Punch ta kasar Najeriya ya nuna mana cewa, ya kamata a nuna karin imani, yayin da ake kula da wasu abubuwan gargajiya.

 

Hakika ci gaban zaman al’umma ya kan sa a kara darajantar abubuwa na gargajiya. A wannan fanni za mu iya duba misali na kasar Sin. A baya, lokacin da kasar ta zama karkashin hare-haren da wasu kasashe masu karfi suka kai mata, da fuskantar danniya a fannin tattalin arziki, da kutsa kai ta fuskar al’adu, Sinawa sun tantace al’adunta na gargajiya bisa kwatantawa da na kasashen yamma cikin zurfi, har ma sun yi la’akari da maye gurbin bakaken Sinanci da haruffan Turanci, don tabbatar da saukin rubutawa a lokacin. Sai dai a kasar Sin ta wannan zamani, mutanen kasar na kokarin kare wurare masu tarihi, da nazari a kansu, da gadon fasahohin al’adu. Yayin da matasa ke kallon tufafi, da kide-kide, da sauran alamu masu salon gargajiya a matsayin abubuwa masu farin jini. Kana duk wani birnin kasar na kokarin raya gidajen ajiyar kayayyakin tarihi, da tsoffin tituna da ungwanni, don nuna tarihi da al’adu na musamman da yake da su.

 

To amma ko mene ne ya sa ake darajantar al’adun gargajiya? Saboda asalin tunanin wata kasa yana cikin al’adunta na gargajiya. Dole ne a yi nazari kan al’adu da tunani na gargajiya, domin ta haka ne za a iya samun wata turbar raya kasa mai dacewa. Misali, manufar zamanantarwa ta kasar Sin ta kunshi bangaren samun jituwa tsakanin dan Adam da muhallin halittu, sai dai asalin bangaren shi ne tunanin Taoism na kasar, na ”duk wani abu da ni a hade suke.” Ban da haka, yadda tunanin zamanantarwa na kasar Sin ke dora muhimmanci kan tabbatar da wadatar daukacin al’umma, shi ma ya samu asalinsa ne daga tunanin gargajiyar kasar Sin na tabbatar da daidaituwa tsakanin al’umma.

 

Ban da haka, yadda ake kokarin kare al’adun gargajiya da raya shi, yana da amfani na musamman ga yunkurin warware matsalolin da duniyarmu ke fuskantar. Tun fil azal, Sinawa sun jaddada muhimmancin tsarin kasancewar duniya karkashin mallakar daukacin kasashe da al’ummun duniya. Saboda haka a ganin kasar, kamata ya yi, a samu daidaito da zumunta tsakanin mabambantan al’ummu. Wannan ra’ayi ya zama daya da tunanin Ubuntu dake yaduwa a nahiyar Afirka, wanda ya jaddada bukatar samun kauna, da huldar cude-ni-in-cude-ka tsakanin mutane.

 

A wannan zamanin da muke ciki, wadannan tunanin gargajiya na Sin da Afirka sun zama matsaya daya ta raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya, wanda ya tabbatar da yiwuwar kawo karshen rikici da nuna bambanci, da kare zaman lafiya da yanayin ci gaba a duniya.

 

A zahiri, ta hanyar dogaro da kai, da kokarin kare al’adun gargajiya, da cudanya tsakanin mabambantan al’adu, za a samar wa duniya da daukacin dan Adam karin abubuwa masu yakini, da tabbatar da makomarsu mai haske. (Bello Wang)

gatari
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
gatari
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Matatar dangote

Ba Za A Yi Layin Man Fetur Ba Idan 'Yan Kasuwa Suka Mayar Da Hankali Kan Matatarmu - Ɗangote 

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.