Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

Gwamna Bagudu Ya Je Ta’aziyar ’Yan Nijar Da Ruwa Ya Cinye

by Tayo Adelaja
September 19, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Umar Faruk, Birnin-kebbi

Gwamnan Jihar kebbi Sanata Abubakar Atiku Bagudu ya kai Gaisuwar Ta’aziya ga Shugaban kasar Nijar Muhammadu Yusuf amadadin Shugaban kasa Nijeriya Muhammad Buhari, a fadar Gwamnatin jamhuriyar Nijar da ke a Niyame a ranar Lahadi 17 ga watan Satumbar 2017.

Sanata Abubakar Bagudu ya samu tarba mai kyau daga takwaransa Gwamnan Jihar Dosso, Alhaji Musa Usman a garin na Dosso, bayan yada zango a garin na Dosso, Gwamna Musa Usman ya jagoranci tawagar Gwamnan na Jihar Kebbi zuwa fadar Shugaban kasar Nijar domin mika gaisuwar ta’aziya Ga Shugaban kasar Nijar Muhammad Yusuf amadadin Shugaban Muhammad Buhari kan bala’in hadarin jirgin ruwa da ya shafi ‘yan kasuwar, har  mutum 100 na garin Gaya a cikin yankin Dosso jamhuriyar Nijar a makon da ya gabata. Wadanda ke kan hanyarsu ta zuwa kasuwa a garin LOLO ta Jihar kebbi.

A jawabinsa na Ta’aziya Ga Shugaban kasar Nijar,  Gwamna Abubakar Atiku Bagudu ya ce ‘Mun zo ne wannan fadar Gwamnatin Nijar domin na wakilci Shugaban kasar Muhammad Buhari kamar yadda ya umurce ni da in zo domin mika ta’aziya ga gwamnatin Nijar, iyalan mamatan da kuma al’ummar kasar Nijar baki daya. Kan babban rashin da kuka yi na ‘yan uwanku, kuma ‘yan kasuwarku da suka samu hadarin Jirgin ruwa a kan hanyarsu ta zuwa kasuwar LOLO da ke cikin karamar hukumar mulki ta Bagudo a jihar kebbin Nijeriya.

Da yake  jawabinsa na godiya ga Gwamnatin Nijeriya da kuma  Gwamnatin jihar Kebbi, Shugaban kasar Nijar, Muhammadu Yusufu ya bayyana jin dadinsa kan irin halin kulawa  da soyaya da ke tsakanin kasashen biyu.

Ya ce: “Ko a lokacin da abin ya faru Shugaban Kasar Nijeriya, Muhammad Buhari ya kira ni a wayarsa ta hannu, ya yi min ta’aziyya. Kuma ya fada min cewa duk da haka zai turo da wakilansa zuwa Jamhuriyar Nijar, domin su yi mana gaisuwar ta’aziya.”

SendShareTweetShare
Previous Post

Sanata Ali Ndume: Dan Siyasa Mai Tagomashin Da Ya Dade Yana Jan Zaren Sa

Next Post

Kamfanin Dangote Zai Dauki Jan Ragamar Kamfanin Suminti Dake Afirka Ta Kudu

RelatedPosts

Babandede Ya Yi Gargadi A Kan Daukan Aiki Na Bogi Da Sunan NIS

Sauye-sauye Masu Ma’ana A Sashen Fasfo Na Hukumar Shige Da Ficen Nijeriya

by Yahuzajere
1 day ago
0

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS), karkashin...

An Gabatar Da Huduba Kan Ramadan A Babban Masallacin Jos

An Gabatar Da Huduba Kan Ramadan A Babban Masallacin Jos

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Daga Mohammed Ahmed Baba, Jos A ranar Juma'ar nan ne...

Yadda Tu’amalli Da Kayan Maye Ke Shafar Lafiyar Matasa Maza Da Mata  – Margaret

Yadda Tu’amalli Da Kayan Maye Ke Shafar Lafiyar Matasa Maza Da Mata  – Margaret

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Uwargida  Margaret  Juliu, sananniyar ce a jihar Kaduna,  musamman wajen fadakar...

Next Post

Kamfanin Dangote Zai Dauki Jan Ragamar Kamfanin Suminti Dake Afirka Ta Kudu

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version