ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Bagudu Ya Kaddamar Da Rabon Tallafin Miliyan 500 Na Shirin KB CARES

by Umar Faruk
3 years ago
Bagudu

Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Abubakar Atiku Bagudu, ya kaddamar da rabon sama da Naira miliyan 500 ga mutane sama da 4,000 da za su ci gajiyar shirin nan na KB CARES a jihar.

A karkashin shirin na hadin guiwa tsakanin gwamnatin Jihar Kebbi da Gwamnatin Tarayya a karkashin Muhammadu Buhari, ‘yan kasuwa 1,950 ne za su ci gajiyar shirin da za su samu Naira dubu 20,000 a wata biyu har na tsawon watanni 24.

  • Lauyoyin Arewa Sun Zargi EFCC Da Nuna Wariya Kan Wadanda Ake Zargi Da Badakalar Kudade
  • Peng Liyuan Ta Ziyarci Dakin Adana Kayan Tarihi Na Fasaha Na Birnin Ayutthaya Na Thailand

Da yake jawabi a wajen taron, Bagudu ya kuma yi magana kan shirin NG-CARES da cewa wani shiri ne na shiga tsakanin Bankin Duniya, Gwamnatin Tarayya da kuma gwamnatocin Jihohi ga al’umma da kuma ‘yan kasuwa a duk fadin Kasar nan.

ADVERTISEMENT

A cewar Bagudu, shirin an yi shi ne don rage tasirin cutar Korona ta hanyar zaman gida da ya biyo bayan barkewar cutar a duniya ciki har da Nijeriya.

Gwamnan, ya ce zaman gidan ya sanya mutanen duniya sun kasance a gida ba tare da samun damar yin duk wani aiki mai ma’ana na zamantakewa da gudanar da ayyukansu ta hanyar rashin habaka tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

Haka zalika, ya kara da cewa, “An raba shirin zuwa sassa da dama inda manoma da dama suka samu takin zamani da kayan masarufi da sinadarai da sauran kayayyakin aiki gona a kyauta.”

Gwamnan dai ya kuma ce taron na musamman ne domin kaddamar da wasu manyan tallafi guda biyu ga al’ummar jihar.

Har-ila-yau Gwamna ya ce, “A karkashin tsarin musayar al’umma, kasa da 1,9500 ne za a bai wa daga N100,000 zuwa N120,000, sau daya. Haka kuma kudaden na wannan fanni sun riga sun kasance a bankunan kasuwanci a fadin jiha kuma an fara raba kudaden.”

Shi ma da yake nasa jawabin kwamishinan kasafin kudi da tsare-tsare na tattalin arziki, Dakta Abba Sani Kalgo ya yaba wa kokarin Gwamna Bagudu na ganin an samu nasarar aiwatar da shirin.

Ya kuma bayyana cewa gwamnan ya ci gaba da jajircewa wajen inganta rayuwar al’ummar jihar.

A cewarsa, “Bayan kaddamar da shirin za a raba sama da naira miliyan 400 zuwa ga mutane 1,950 yayin da wasu kananan ayyuka aka gudanar a kananan hukumomi 13.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
Manyan Labarai

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane
Labarai

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle
Labarai

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Next Post
Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Su Ne Muradun Sinawa

Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Su Ne Muradun Sinawa

LABARAI MASU NASABA

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

November 13, 2025
Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

November 13, 2025
Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

November 13, 2025
Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

November 13, 2025
‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.