• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Bagudu Ya Kaddamar Da Rabon Tallafin Miliyan 500 Na Shirin KB CARES

by Umar Faruk
3 years ago
Bagudu

Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Abubakar Atiku Bagudu, ya kaddamar da rabon sama da Naira miliyan 500 ga mutane sama da 4,000 da za su ci gajiyar shirin nan na KB CARES a jihar.

A karkashin shirin na hadin guiwa tsakanin gwamnatin Jihar Kebbi da Gwamnatin Tarayya a karkashin Muhammadu Buhari, ‘yan kasuwa 1,950 ne za su ci gajiyar shirin da za su samu Naira dubu 20,000 a wata biyu har na tsawon watanni 24.

  • Lauyoyin Arewa Sun Zargi EFCC Da Nuna Wariya Kan Wadanda Ake Zargi Da Badakalar Kudade
  • Peng Liyuan Ta Ziyarci Dakin Adana Kayan Tarihi Na Fasaha Na Birnin Ayutthaya Na Thailand

Da yake jawabi a wajen taron, Bagudu ya kuma yi magana kan shirin NG-CARES da cewa wani shiri ne na shiga tsakanin Bankin Duniya, Gwamnatin Tarayya da kuma gwamnatocin Jihohi ga al’umma da kuma ‘yan kasuwa a duk fadin Kasar nan.

A cewar Bagudu, shirin an yi shi ne don rage tasirin cutar Korona ta hanyar zaman gida da ya biyo bayan barkewar cutar a duniya ciki har da Nijeriya.

Gwamnan, ya ce zaman gidan ya sanya mutanen duniya sun kasance a gida ba tare da samun damar yin duk wani aiki mai ma’ana na zamantakewa da gudanar da ayyukansu ta hanyar rashin habaka tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Haka zalika, ya kara da cewa, “An raba shirin zuwa sassa da dama inda manoma da dama suka samu takin zamani da kayan masarufi da sinadarai da sauran kayayyakin aiki gona a kyauta.”

Gwamnan dai ya kuma ce taron na musamman ne domin kaddamar da wasu manyan tallafi guda biyu ga al’ummar jihar.

Har-ila-yau Gwamna ya ce, “A karkashin tsarin musayar al’umma, kasa da 1,9500 ne za a bai wa daga N100,000 zuwa N120,000, sau daya. Haka kuma kudaden na wannan fanni sun riga sun kasance a bankunan kasuwanci a fadin jiha kuma an fara raba kudaden.”

Shi ma da yake nasa jawabin kwamishinan kasafin kudi da tsare-tsare na tattalin arziki, Dakta Abba Sani Kalgo ya yaba wa kokarin Gwamna Bagudu na ganin an samu nasarar aiwatar da shirin.

Ya kuma bayyana cewa gwamnan ya ci gaba da jajircewa wajen inganta rayuwar al’ummar jihar.

A cewarsa, “Bayan kaddamar da shirin za a raba sama da naira miliyan 400 zuwa ga mutane 1,950 yayin da wasu kananan ayyuka aka gudanar a kananan hukumomi 13.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Next Post
Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Su Ne Muradun Sinawa

Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Su Ne Muradun Sinawa

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.