ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Bagudu Ya Kaddamar Da Rabon Tallafin Miliyan 500 Na Shirin KB CARES

by Umar Faruk
4 years ago
Bagudu

Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Abubakar Atiku Bagudu, ya kaddamar da rabon sama da Naira miliyan 500 ga mutane sama da 4,000 da za su ci gajiyar shirin nan na KB CARES a jihar.

A karkashin shirin na hadin guiwa tsakanin gwamnatin Jihar Kebbi da Gwamnatin Tarayya a karkashin Muhammadu Buhari, ‘yan kasuwa 1,950 ne za su ci gajiyar shirin da za su samu Naira dubu 20,000 a wata biyu har na tsawon watanni 24.

  • Lauyoyin Arewa Sun Zargi EFCC Da Nuna Wariya Kan Wadanda Ake Zargi Da Badakalar Kudade
  • Peng Liyuan Ta Ziyarci Dakin Adana Kayan Tarihi Na Fasaha Na Birnin Ayutthaya Na Thailand

Da yake jawabi a wajen taron, Bagudu ya kuma yi magana kan shirin NG-CARES da cewa wani shiri ne na shiga tsakanin Bankin Duniya, Gwamnatin Tarayya da kuma gwamnatocin Jihohi ga al’umma da kuma ‘yan kasuwa a duk fadin Kasar nan.

ADVERTISEMENT

A cewar Bagudu, shirin an yi shi ne don rage tasirin cutar Korona ta hanyar zaman gida da ya biyo bayan barkewar cutar a duniya ciki har da Nijeriya.

Gwamnan, ya ce zaman gidan ya sanya mutanen duniya sun kasance a gida ba tare da samun damar yin duk wani aiki mai ma’ana na zamantakewa da gudanar da ayyukansu ta hanyar rashin habaka tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

Haka zalika, ya kara da cewa, “An raba shirin zuwa sassa da dama inda manoma da dama suka samu takin zamani da kayan masarufi da sinadarai da sauran kayayyakin aiki gona a kyauta.”

Gwamnan dai ya kuma ce taron na musamman ne domin kaddamar da wasu manyan tallafi guda biyu ga al’ummar jihar.

Har-ila-yau Gwamna ya ce, “A karkashin tsarin musayar al’umma, kasa da 1,9500 ne za a bai wa daga N100,000 zuwa N120,000, sau daya. Haka kuma kudaden na wannan fanni sun riga sun kasance a bankunan kasuwanci a fadin jiha kuma an fara raba kudaden.”

Shi ma da yake nasa jawabin kwamishinan kasafin kudi da tsare-tsare na tattalin arziki, Dakta Abba Sani Kalgo ya yaba wa kokarin Gwamna Bagudu na ganin an samu nasarar aiwatar da shirin.

Ya kuma bayyana cewa gwamnan ya ci gaba da jajircewa wajen inganta rayuwar al’ummar jihar.

A cewarsa, “Bayan kaddamar da shirin za a raba sama da naira miliyan 400 zuwa ga mutane 1,950 yayin da wasu kananan ayyuka aka gudanar a kananan hukumomi 13.”

Bagudu
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Nijeriya Da Jamhuriyar Benin Za Su Sassauta Tsanantawa A Kan Iyakokinsu Ga ‘Yan Kasuwa
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Hajjin Bana: Shettima Zai Kaddamar Da Jirgin Farko Na Maniyyata 430 A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Jami’an Tsaro sun Ceto Mata Biyu da aka Yi Garkuwa da Su A Kebbi

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Su Ne Muradun Sinawa

Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Su Ne Muradun Sinawa

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.