ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara

Za a samar da sashen da zai kunshi gadaje 200

by Leadership Hausa
1 year ago
Asibiti

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya ƙaddamar da aikin sake gina babban asibitin Ƙaramar Hukumar Talata Mafara da samar da katafaren ginin da zai ɗauki gadaje 200.

A yayin ƙaddamarwar, gwamnan ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na inganta kiwon lafiya a jihar, tare da bayyana irin rawar da manyan asibitoci ke takawa a fannin kiwon lafiya.

Mallam Yahaya Abdulkarim, tsohon gwamnan Jihar Sakkwato ne babban baƙo na musamman a wajen bikin ƙaddamarwar.

ADVERTISEMENT

Gwamna Dauda Lawal, ya bayyana damuwarsa kan yadda aka yi watsi da babban asibitin Talatan Mafara, inda ya nuna cewa asibitin na fama da rashin isassun kayan aikin jinya da kuma rashin kyawun ababen more rayuwa a tsawon shekaru.

Ya ce gwamnatocin baya sun yi watsi da harkar kiwon lafiya gaba ɗaya, wanda hakan ya sa gwamnatinsa ta fara aiwatar da aikin gyara fannin.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

“Da yardar Allah yau na zo ne domin cika alƙawarin da na ɗauka a watannin baya lokacin da na ziyarci wannan asibiti da jami’ar jihar. Bisa la’akari da halin da ake ciki a wannan cibiyar kiwon lafiya, na yi alƙawarin gudanar da aikin sake gina shi gaba ɗaya don samar da babban asibitin da ya dace da babban gari kamar Talata Mafara.

“Gwamnatinmu ta ba da fifiko wajen farfaɗo da ababen more rayuwa a matsayin muhimmin ginshiƙin ajandar kawo sauyi. Mun sanya ilimi da kiwon lafiya a kan gaba, tare da sanin matsayinsu wajen ci gaban al’umma. Wannan asibiti ɗaya ne daga cikin wurare da yawa da ake ginawa don samar da yanayi mai kyau wajen samar da nagartaccen ayyukan kiwon lafiya.

  • Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago

 

“Gwamnatinmu ta tsaya tsayin daka wajen sanya hannun jari a fannin kiwon lafiya, tare da fahimtar muhimmiyar rawar da manyan asibitocin ke takawa a tsarin samar da lafiya. Suna aiki a matsayin muhimman hanyoyin da suka haɗa cibiyoyin Kula da Lafiya na Farko da Manyan Cibiyoyin Kiwon Lafiya.

“Aikin da muke ƙaddamarwa a yau ya ƙunshi gina asibiti mai ɗaukar gadaje 200 tare da samar da kayan aiki na zamani domin inganta lafiyar al’umma.

“Ya haɗa da gine-gine kamar haka: Wuraren zaman jira, sashin bayanai da asusun ajiya, sashen kula da yara, ɗakin jinya na maza, ɗakin jinya na mazan da aka yi wa tiyata, ɗakin gwaje-gwaje, ɗakin tiyata, ɗakin gwaje-gwajen haƙori, ɗakin karɓar magani, ɗakin jinya na matan da aka yi wa tiyata, ɗakin jinya na mata, sashen ENT. Ɗakunan haihuwa guda biyu tare da ofishin babbar mai karɓar haihuwa, ɗakin wankin ciwo, ɗakin zaman ma’aikatan jinya, ofishin Babban Manajan Daraktan Kiwon Lafiya na asibitin tare da ofishin sakatarensa, ofishin likitan haƙori, ɗakin canja kaya na mata, ɗakunan ganin likita guda biyar, ɗakin ICU, rukunin na’urar X-ray, sashen kai marasa lafiya na gaggawa ‘Accident & Emergency (A&E)’, sashen kula da masu juna biyu, wurin cin abinci, da ofishin matron.

“Za a kammala shi cikin watanni shida, inda kamfanin Abdulwahab Razaq Memorial Ltd ya kasance a matsayin ɗan kwangilar. A halin da ake ciki, abin farin ciki ne na musamman na gayyato babban baƙon mu, mai girma tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato, Malam Yahaya Abdulkarim, Magajin Rafin Sokoto, domin ƙaddamar da aikin gina wannan asibiti a hukumance.”

Tun da farko, tsohon gwamnan Jihar Sakkwato, Malam Yahaya Abdulkarim, ya yaba wa gwamna Dauda Lawal bisa bai wa ɓangaren kiwon lafiya fifiko a cikin ayyukan da gwamnatinsa ta sa gaba. “Na yi mamakin lokacin da gwamnan ya shaida min cewa an riga an sayo dukkan kayan aikin da za a yi amfani da su a Babban Asibitin, wannan abin yabawa ne matuƙa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
Rushewar Gine-gine Ta Yi Sanadiyar Rasuwar Mutane Fiye Da 90 A Shekara Daya

Rushewar Gine-gine Ta Yi Sanadiyar Rasuwar Mutane Fiye Da 90 A Shekara Daya

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.