• Leadership Hausa
Monday, March 27, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Inuwa Ya Amince Da Biyan Giratuti Na Naira Biliyan 1.3 Ga Ma’aikatan Kananan Hukumomi

by Khalid Idris Doya
2 months ago
in Labarai
0
2023: Zarge-zargen PDP A Kaina Soki-burutsu Ne Kawai – Gwamnan Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya amince da sakin fiye da naira biliyan 1 da miliyan 300 don biyan bashin ma’aikatan kananan hukumomin da suka yi ritaya. 

 

An biya ma’aikatan lananan hukumomi da suka yi ritaya giratuti na karshe ne a 2011.

  • Mun Dandana Kudarmu A 2022, In Ji ‘Yan Kasuwa A Jihar Gombe

Gwamnan ya kuma amince da karin girma nan take ga ma’aikatan kananan hukumomi dubu 26, da 85 a fadin kananan hukumomi 11 na jihar.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

Daga cikin adadin ma’aikatan da aka karawa girman, dubu 6 da 738 ma’aikata ne na kananan hukumomi, yayin da dubu 16 da 739 kuma malaman LEA, sai dubu 2 da 608 ma’aikatan cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko.

 

Kwamishinan kananan hukumomi da masarautu, Hon. Ibrahim Dasuki Jalo ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa, ya bayyana cewar, lokaci na karshe da aka karawa malamai girma a jihar shi ne a shekarar 2009 yayin da aka fara aiwatar da shi a 2014.

 

Shi ma da ya ke jawabi, kwamishinan kudi da bunkasa tattalin arziki, Malam Muhammad Gambo Magaji ya mika takardar amincewar gwamnan jihar na Naira biliyan 1 da miliyan 700 don biyan basussukan ma’aikatan da suka yi ritaya a jihar a shekarar 2017.

 

“Biyan bashin ma’aikatan da suka yi ritaya daga gwamnatin Inuwa ya lakume kimanin Naira biliyan 7 da miliyan 900. Idan dai za a iya tunawa, a baya Gwamna Inuwa ya biya bashin kudaden giratutin wadanda suka yi ritaya a jihar na shekarun 2014, da 2015 da 2016 sai kuma yanzu na shekarar 2017, yayin da jimillar kudaden da aka biya a matakin jiha ya kai Naira biliyan 6 da miliyan 600.”

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bangaren Cinikayyar Hidimomi A Kasar Sin Ya Karu Da 12.9% A 2022

Next Post

IMF: Tattalin Arzikin Sin Zai Karu Zuwa 5,2% A Bana

Related

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba
Labarai

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

3 hours ago
Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara
Labarai

Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

5 hours ago
2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe
Labarai

2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

7 hours ago
SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa
Labarai

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

8 hours ago
DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci
Labarai

DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

9 hours ago
PDP Ta Dakatar Da Tsofaffin Ministoci 2 Da Wasu 5 Kan Yi Wa Jam’iyyar Zagon-Kasa
Labarai

PDP Ta Dakatar Da Shugabanta Na Kasa Kan Zargin Yi Wa Jam’iyyar Adawa Aiki

18 hours ago
Next Post
IMF: Tattalin Arzikin Sin Zai Karu Zuwa 5,2% A Bana

IMF: Tattalin Arzikin Sin Zai Karu Zuwa 5,2% A Bana

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

March 27, 2023
Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

March 27, 2023
2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

March 27, 2023
SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

March 27, 2023
DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

March 27, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 3 A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 5

March 27, 2023
PDP Ta Dakatar Da Tsofaffin Ministoci 2 Da Wasu 5 Kan Yi Wa Jam’iyyar Zagon-Kasa

PDP Ta Dakatar Da Shugabanta Na Kasa Kan Zargin Yi Wa Jam’iyyar Adawa Aiki

March 26, 2023
Amurka Ta Sake Zargin Kasar Sin Kan Asalin Kwayar Cutar COVID-19 Domin Yunkurin Siyasa

Amurka Ta Sake Zargin Kasar Sin Kan Asalin Kwayar Cutar COVID-19 Domin Yunkurin Siyasa

March 26, 2023
Za A Fuskanci Dumamar Yanayi A Sokoto Da Zamfara Da Sauran Jihohi

Za A Fuskanci Dumamar Yanayi A Sokoto Da Zamfara Da Sauran Jihohi

March 26, 2023
2023: Za A Fara Kidayar Jama’a Da Gidaje 3, Ga Watan Mayu – Gwamnati

2023: Za A Fara Kidayar Jama’a Da Gidaje 3, Ga Watan Mayu – Gwamnati

March 26, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.