• English
  • Business News
Thursday, July 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

by Hussein Yero
4 hours ago
in Labarai
0
Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya fara raba tallafin kuɗi ga ɗalibai ‘yan mata 8,225 da ke cikin ƙananan hukumomi 14 na jihar.

An fara rabon ne a ranar Laraba a ɗakin taro na Garba Nadama da ke sakatariyar JB Yakubu a Gusau, ƙarƙashin shirye-shiryen ACReSAL da AGILE.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet
  • Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, an zaɓi waɗannan daliban ne duba da yanayin iyayensu masu ƙaramin ƙarfi domin a taimaka musu su ci gaba da karatu.

Kowace ɗaliba za ta karɓi Naira 40,000 a zangon farko, sannan a zangon karatu na biyu da na uku, za a ƙara mata Naira 10,000, hakan na nufin kowace za ta samu Naira 60,000 a shekara.

An riga an ware Naira miliyan 132 domin rukuni na farko, kuma an fara shirin rukuni na biyu.

Labarai Masu Nasaba

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

A wajen taron, Gwamna Lawal ya bayyana cewa ƙarƙashin shirin ACReSAL, an raba tallafi ga mutum 500 a Gusau, Bungudu da Ƙaura Namoda, domin inganta harkar noma da farfaɗo da tattalin arziƙi.

Ya ƙara da cewa, “Wannan tallafin zai ci gaba da yawo a faɗin jihar, kuma mutane da dama za su ci gajiyarsa. Idan aka yi amfani da damar yadda ya kamata, to za a samu ci gaba sosai.”

Gwamnan ya bayyana cewa ilimi na daga cikin abubuwan da gwamnatinsa ta fi mayar da hankali a kai, musamman na ‘yan mata.

Ya ce, “Mun ɗauki matakai na kawar da duk wani cikas da zai hana ‘yan mata su kammala karatunsu. Idan ka ilmantar da yarinya, ka ilmantar da al’umma gaba ɗaya.”

Ya yaba wa ma’aikatar muhalli da ta ilimi saboda jajircewarsu wajen ganin shirin ya yi nasara.

A ƙarshe, ya roƙi waɗanda suka amfana da tallafin da su yi amfani da shi yadda ya kamata domin amfanin kansu da iyalansu da kuma al’umma baki ɗaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ƊalibaiTallafiZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

Next Post

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

Related

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa
Labarai

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

2 hours ago
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC
Manyan Labarai

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

6 hours ago
Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila
Manyan Labarai

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

8 hours ago
Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu
Manyan Labarai

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

9 hours ago
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi
Labarai

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

17 hours ago
Next Post
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

LABARAI MASU NASABA

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

July 17, 2025
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

July 17, 2025
Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

July 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

July 17, 2025
Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

July 17, 2025
Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

July 17, 2025
Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

July 17, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

July 16, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

July 16, 2025
Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.