• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

by Hussein Yero
3 months ago
Tallafi

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya fara raba tallafin kuɗi ga ɗalibai ‘yan mata 8,225 da ke cikin ƙananan hukumomi 14 na jihar.

An fara rabon ne a ranar Laraba a ɗakin taro na Garba Nadama da ke sakatariyar JB Yakubu a Gusau, ƙarƙashin shirye-shiryen ACReSAL da AGILE.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet
  • Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, an zaɓi waɗannan daliban ne duba da yanayin iyayensu masu ƙaramin ƙarfi domin a taimaka musu su ci gaba da karatu.

Kowace ɗaliba za ta karɓi Naira 40,000 a zangon farko, sannan a zangon karatu na biyu da na uku, za a ƙara mata Naira 10,000, hakan na nufin kowace za ta samu Naira 60,000 a shekara.

An riga an ware Naira miliyan 132 domin rukuni na farko, kuma an fara shirin rukuni na biyu.

LABARAI MASU NASABA

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

A wajen taron, Gwamna Lawal ya bayyana cewa ƙarƙashin shirin ACReSAL, an raba tallafi ga mutum 500 a Gusau, Bungudu da Ƙaura Namoda, domin inganta harkar noma da farfaɗo da tattalin arziƙi.

Ya ƙara da cewa, “Wannan tallafin zai ci gaba da yawo a faɗin jihar, kuma mutane da dama za su ci gajiyarsa. Idan aka yi amfani da damar yadda ya kamata, to za a samu ci gaba sosai.”

Gwamnan ya bayyana cewa ilimi na daga cikin abubuwan da gwamnatinsa ta fi mayar da hankali a kai, musamman na ‘yan mata.

Ya ce, “Mun ɗauki matakai na kawar da duk wani cikas da zai hana ‘yan mata su kammala karatunsu. Idan ka ilmantar da yarinya, ka ilmantar da al’umma gaba ɗaya.”

Ya yaba wa ma’aikatar muhalli da ta ilimi saboda jajircewarsu wajen ganin shirin ya yi nasara.

A ƙarshe, ya roƙi waɗanda suka amfana da tallafin da su yi amfani da shi yadda ya kamata domin amfanin kansu da iyalansu da kuma al’umma baki ɗaya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba
Labarai

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

October 18, 2025
Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Next Post
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

LABARAI MASU NASABA

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

October 18, 2025
Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

October 18, 2025
Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.