• English
  • Business News
Sunday, September 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Raba Kayan Karatu 408,137 Ga Makarantun Gwamnatin Zamfara

by Sulaiman
2 hours ago
in Labarai
0
Gwamna Lawal Ya Raba Kayan Karatu 408,137 Ga Makarantun Gwamnatin Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal na jihar Zamfara ya sayo kayan koyo da koyarwa har guda 408,137 domin rabawa ga makarantun gwamnati a faɗin jihar.

 

An gudanar da bikin rabon ne a ranar Juma’a a Cibiyar Horar da Malamai ta TTDC da ke hanyar Bypass a Gusau.

  • Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima
  • Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa rabon bai tsaya ga littattafai kaɗai ba; an shi ne domin tabbatar da Zamfara ta hau kan turbar farfaɗowa, sabuntawa, da ci gaba ta hanyar ilimi.

 

Labarai Masu Nasaba

An Cafke Wani Magidanci Da Lafin Sojan Gona A Katsina

Wata Mahanga Ta Daban Ta Kallon Ayyukan Ta’addanci

Sanarwar ta ƙara da cewa, an bayar da ƙarin kayayyakin da za a raba a matsayin tallafin ne daga Hukumar Kula da Ilimi ta Duniya (UBEC) da UNICEF.

 

A jawabinsa a wajen taron, Gwamna Lawal ya sake nanata cewa gwamnatinsa ta zo ne da aikin ceto da sake gina jihar.

 

Ya ce: “Tun da farko mun gane cewa hanya mafi inganci wajen dawo da Zamfara kan turba ita ce saka hannun jari a zukatan al’ummarmu.

 

“A yau, a cikin wannan alƙawari, na yi farin cikin sanar da raba kayayyakin koyo da koyarwa 408,137 da gwamnatin jihar Zamfara ta sayo kai-tsaye.

 

“Wannan shi ne ɗaya daga cikin mafi girma na zuba jari a cikin albarkatun koyarwa da jiharmu ta taba gani. Ya nuna imanin mu cewa malamai ba za su iya yin nasara ba tare da kayan aikin da suka dace ba, kuma yara ba za su iya koyo ba tare da isassun kayan karatu ba.

 

“Amma wannan ƙoƙarin ba namu kaɗai ba ne, muna godiya tare da haɗin gwiwar Hukumar Kula da Ilimin Bai-ɗaya (UBEC), wadda ta samar da kayayyakin koyo da koyarwa 77,609 domin ƙara wa shirin gwamnatin jiharmu.

 

“Gudunmawar da suke bayarwa ta nuna cewa ana samun ci gaba mai kyau idan gwamnatoci a matakai daban-daban suka yi aiki tare, tare da haɗin kan jama’a.

 

“Muna gode wa abokan aikinmu na ci gaba, musamman UNICEF, da suka samar da littattafai masu muhimmanci 5,000. Waɗannan litattafan za su ba yaranmu ilimi mai muhimmanci na muhalli da kuma ilimin tattalin arziki, tare ba su ƙarin haske kan yadda duniya take da canjin yanayi.

 

“Kowanne daga cikin waɗannan kayan da jihar ta sayo, da gudunmawar UBEC, da tallafin UNICEF, na da ma’anarsa. Amma tare, sun ba da labari ɗaya mai ƙarfi, Zamfara ta zabi hanyar ilimi a matsayin ginshiƙin sake gina al’umma.”

 

Gwamna Lawal ya kuma yaba wa malaman Zamfara bisa sadaukarwar da suke yi a fannin ilimi.

 

“Dole ne na ɗauki lokaci don yaba wa malamanmu, babu wani abin da zai iya maye gurbin sadaukarwar malamin da ke zaburar da ɗalibai a kullum. Waɗannan albarkatun da muke rarrabawa za su kasance masu ma’ana ne kawai idan an yi amfani da su sosai ta hanyar masu sha’awar ilmantarwa.

 

“Ga iyaye, don Allah ku gane muhimmiyar rawar da ku ke takawa a ilimin yaranku. Littafi shi kaɗai ba ya isa ba tare da ƙarfafawa a gida ba. Ilimi yana farawa ne daga gida, tarbiyya da jagoranci ke kafa tushen nasara. Ina roƙon ku da ku bai wa makaranta muhimmanci, kula da ayyukan ilimi, kuma ku tunatar da yaranku cewa makomarsu ta dogara ne akan sadaukarwarsu wajen koyon karatu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Ƙasashen Musulmi Za Su Iya Kafa Ƙawancen Tsaro Don Tunkarar Abokan Gaba?

Next Post

Wata Mahanga Ta Daban Ta Kallon Ayyukan Ta’addanci

Related

Gwamna lawal
Labarai

An Cafke Wani Magidanci Da Lafin Sojan Gona A Katsina

23 minutes ago
Gwamna lawal
Manyan Labarai

Wata Mahanga Ta Daban Ta Kallon Ayyukan Ta’addanci

1 hour ago
Ko Ƙasashen Musulmi Za Su Iya Kafa Ƙawancen Tsaro Don Tunkarar Abokan Gaba?
Labarai

Ko Ƙasashen Musulmi Za Su Iya Kafa Ƙawancen Tsaro Don Tunkarar Abokan Gaba?

2 hours ago
Digirin Bogi Aka Bai Wa Mawaƙi Rarara A Nijeriya – Jami’ar EAU
Manyan Labarai

Digirin Bogi Aka Bai Wa Mawaƙi Rarara A Nijeriya – Jami’ar EAU

4 hours ago
Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima

6 hours ago
Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna
Labarai

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

16 hours ago
Next Post
Gwamna lawal

Wata Mahanga Ta Daban Ta Kallon Ayyukan Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Gwamna lawal

An Cafke Wani Magidanci Da Lafin Sojan Gona A Katsina

September 21, 2025
Gwamna lawal

Wata Mahanga Ta Daban Ta Kallon Ayyukan Ta’addanci

September 21, 2025
Gwamna Lawal Ya Raba Kayan Karatu 408,137 Ga Makarantun Gwamnatin Zamfara

Gwamna Lawal Ya Raba Kayan Karatu 408,137 Ga Makarantun Gwamnatin Zamfara

September 21, 2025
Ko Ƙasashen Musulmi Za Su Iya Kafa Ƙawancen Tsaro Don Tunkarar Abokan Gaba?

Ko Ƙasashen Musulmi Za Su Iya Kafa Ƙawancen Tsaro Don Tunkarar Abokan Gaba?

September 21, 2025
Digirin Bogi Aka Bai Wa Mawaƙi Rarara A Nijeriya – Jami’ar EAU

Digirin Bogi Aka Bai Wa Mawaƙi Rarara A Nijeriya – Jami’ar EAU

September 21, 2025
Gwamna lawal

Djed Spence: Musulmin Da Ya Fara Bugawa Tawagar Ingila Wasan Ƙwallon Ƙafa A Tarihi

September 21, 2025
Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima

Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima

September 21, 2025
Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO

Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO

September 20, 2025
An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

September 20, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni

September 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.