ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Raba Kayan Karatu 408,137 Ga Makarantun Gwamnatin Zamfara

by Sulaiman
9 months ago
Gwamna lawal

Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal na jihar Zamfara ya sayo kayan koyo da koyarwa har guda 408,137 domin rabawa ga makarantun gwamnati a faɗin jihar.

 

An gudanar da bikin rabon ne a ranar Juma’a a Cibiyar Horar da Malamai ta TTDC da ke hanyar Bypass a Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima
  • Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa rabon bai tsaya ga littattafai kaɗai ba; an shi ne domin tabbatar da Zamfara ta hau kan turbar farfaɗowa, sabuntawa, da ci gaba ta hanyar ilimi.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Sanarwar ta ƙara da cewa, an bayar da ƙarin kayayyakin da za a raba a matsayin tallafin ne daga Hukumar Kula da Ilimi ta Duniya (UBEC) da UNICEF.

 

A jawabinsa a wajen taron, Gwamna Lawal ya sake nanata cewa gwamnatinsa ta zo ne da aikin ceto da sake gina jihar.

 

Ya ce: “Tun da farko mun gane cewa hanya mafi inganci wajen dawo da Zamfara kan turba ita ce saka hannun jari a zukatan al’ummarmu.

 

“A yau, a cikin wannan alƙawari, na yi farin cikin sanar da raba kayayyakin koyo da koyarwa 408,137 da gwamnatin jihar Zamfara ta sayo kai-tsaye.

 

“Wannan shi ne ɗaya daga cikin mafi girma na zuba jari a cikin albarkatun koyarwa da jiharmu ta taba gani. Ya nuna imanin mu cewa malamai ba za su iya yin nasara ba tare da kayan aikin da suka dace ba, kuma yara ba za su iya koyo ba tare da isassun kayan karatu ba.

 

“Amma wannan ƙoƙarin ba namu kaɗai ba ne, muna godiya tare da haɗin gwiwar Hukumar Kula da Ilimin Bai-ɗaya (UBEC), wadda ta samar da kayayyakin koyo da koyarwa 77,609 domin ƙara wa shirin gwamnatin jiharmu.

 

“Gudunmawar da suke bayarwa ta nuna cewa ana samun ci gaba mai kyau idan gwamnatoci a matakai daban-daban suka yi aiki tare, tare da haɗin kan jama’a.

 

“Muna gode wa abokan aikinmu na ci gaba, musamman UNICEF, da suka samar da littattafai masu muhimmanci 5,000. Waɗannan litattafan za su ba yaranmu ilimi mai muhimmanci na muhalli da kuma ilimin tattalin arziki, tare ba su ƙarin haske kan yadda duniya take da canjin yanayi.

 

“Kowanne daga cikin waɗannan kayan da jihar ta sayo, da gudunmawar UBEC, da tallafin UNICEF, na da ma’anarsa. Amma tare, sun ba da labari ɗaya mai ƙarfi, Zamfara ta zabi hanyar ilimi a matsayin ginshiƙin sake gina al’umma.”

 

Gwamna Lawal ya kuma yaba wa malaman Zamfara bisa sadaukarwar da suke yi a fannin ilimi.

 

“Dole ne na ɗauki lokaci don yaba wa malamanmu, babu wani abin da zai iya maye gurbin sadaukarwar malamin da ke zaburar da ɗalibai a kullum. Waɗannan albarkatun da muke rarrabawa za su kasance masu ma’ana ne kawai idan an yi amfani da su sosai ta hanyar masu sha’awar ilmantarwa.

 

“Ga iyaye, don Allah ku gane muhimmiyar rawar da ku ke takawa a ilimin yaranku. Littafi shi kaɗai ba ya isa ba tare da ƙarfafawa a gida ba. Ilimi yana farawa ne daga gida, tarbiyya da jagoranci ke kafa tushen nasara. Ina roƙon ku da ku bai wa makaranta muhimmanci, kula da ayyukan ilimi, kuma ku tunatar da yaranku cewa makomarsu ta dogara ne akan sadaukarwarsu wajen koyon karatu.”

Gwamna lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Sulaiman
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
  • Sulaiman
    Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita
  • Sulaiman
    Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci
Labarai

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Labarai

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Next Post
Gwamna lawal

Wata Mahanga Ta Daban Ta Kallon Ayyukan Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.