ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, September 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Raba Kayan Karatu 408,137 Ga Makarantun Gwamnatin Zamfara

by Sulaiman
12 months ago
Gwamna lawal

Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal na jihar Zamfara ya sayo kayan koyo da koyarwa har guda 408,137 domin rabawa ga makarantun gwamnati a faɗin jihar.

 

An gudanar da bikin rabon ne a ranar Juma’a a Cibiyar Horar da Malamai ta TTDC da ke hanyar Bypass a Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima
  • Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa rabon bai tsaya ga littattafai kaɗai ba; an shi ne domin tabbatar da Zamfara ta hau kan turbar farfaɗowa, sabuntawa, da ci gaba ta hanyar ilimi.

 

LABARAI MASU NASABA

Boko Haram Ta Lalata Makarantu 5,000 A Borno – Zulum

Jami’an Tsaro Sun Ƙaddamar Da Aikin Ceto Limaman Da Aka Sace Bayan Taron APC A Zamfara 

Sanarwar ta ƙara da cewa, an bayar da ƙarin kayayyakin da za a raba a matsayin tallafin ne daga Hukumar Kula da Ilimi ta Duniya (UBEC) da UNICEF.

 

A jawabinsa a wajen taron, Gwamna Lawal ya sake nanata cewa gwamnatinsa ta zo ne da aikin ceto da sake gina jihar.

 

Ya ce: “Tun da farko mun gane cewa hanya mafi inganci wajen dawo da Zamfara kan turba ita ce saka hannun jari a zukatan al’ummarmu.

 

“A yau, a cikin wannan alƙawari, na yi farin cikin sanar da raba kayayyakin koyo da koyarwa 408,137 da gwamnatin jihar Zamfara ta sayo kai-tsaye.

 

“Wannan shi ne ɗaya daga cikin mafi girma na zuba jari a cikin albarkatun koyarwa da jiharmu ta taba gani. Ya nuna imanin mu cewa malamai ba za su iya yin nasara ba tare da kayan aikin da suka dace ba, kuma yara ba za su iya koyo ba tare da isassun kayan karatu ba.

 

“Amma wannan ƙoƙarin ba namu kaɗai ba ne, muna godiya tare da haɗin gwiwar Hukumar Kula da Ilimin Bai-ɗaya (UBEC), wadda ta samar da kayayyakin koyo da koyarwa 77,609 domin ƙara wa shirin gwamnatin jiharmu.

 

“Gudunmawar da suke bayarwa ta nuna cewa ana samun ci gaba mai kyau idan gwamnatoci a matakai daban-daban suka yi aiki tare, tare da haɗin kan jama’a.

 

“Muna gode wa abokan aikinmu na ci gaba, musamman UNICEF, da suka samar da littattafai masu muhimmanci 5,000. Waɗannan litattafan za su ba yaranmu ilimi mai muhimmanci na muhalli da kuma ilimin tattalin arziki, tare ba su ƙarin haske kan yadda duniya take da canjin yanayi.

 

“Kowanne daga cikin waɗannan kayan da jihar ta sayo, da gudunmawar UBEC, da tallafin UNICEF, na da ma’anarsa. Amma tare, sun ba da labari ɗaya mai ƙarfi, Zamfara ta zabi hanyar ilimi a matsayin ginshiƙin sake gina al’umma.”

 

Gwamna Lawal ya kuma yaba wa malaman Zamfara bisa sadaukarwar da suke yi a fannin ilimi.

 

“Dole ne na ɗauki lokaci don yaba wa malamanmu, babu wani abin da zai iya maye gurbin sadaukarwar malamin da ke zaburar da ɗalibai a kullum. Waɗannan albarkatun da muke rarrabawa za su kasance masu ma’ana ne kawai idan an yi amfani da su sosai ta hanyar masu sha’awar ilmantarwa.

 

“Ga iyaye, don Allah ku gane muhimmiyar rawar da ku ke takawa a ilimin yaranku. Littafi shi kaɗai ba ya isa ba tare da ƙarfafawa a gida ba. Ilimi yana farawa ne daga gida, tarbiyya da jagoranci ke kafa tushen nasara. Ina roƙon ku da ku bai wa makaranta muhimmanci, kula da ayyukan ilimi, kuma ku tunatar da yaranku cewa makomarsu ta dogara ne akan sadaukarwarsu wajen koyon karatu.”

Gwamna lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Boko Haram Ta Lalata Makarantu 5,000 A Borno – Zulum
  • Sulaiman
    CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi
  • Sulaiman
    Jami’an Tsaro Sun Ƙaddamar Da Aikin Ceto Limaman Da Aka Sace Bayan Taron APC A Zamfara 
  • Sulaiman
    Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

MASU ALAKA

Boko Haram Ta Lalata Makarantu 5,000 A Borno – Zulum
Labarai

Boko Haram Ta Lalata Makarantu 5,000 A Borno – Zulum

September 14, 2026
Dansanda Ya Ki Karbar Cin Hancin Miliyan 1 Kan Ya Saki Wani Barawon Mutane A Kano
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Ƙaddamar Da Aikin Ceto Limaman Da Aka Sace Bayan Taron APC A Zamfara 

September 14, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom
Labarai

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

September 13, 2026
Next Post
Gwamna lawal

Wata Mahanga Ta Daban Ta Kallon Ayyukan Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Boko Haram Ta Lalata Makarantu 5,000 A Borno – Zulum

Boko Haram Ta Lalata Makarantu 5,000 A Borno – Zulum

September 14, 2026
CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi

CIFTIS Ya Zurfafa Cimma Matsaya Kan Hadin Gwiwar Duniya A Fannin Hidimomi

September 14, 2026
Dansanda Ya Ki Karbar Cin Hancin Miliyan 1 Kan Ya Saki Wani Barawon Mutane A Kano

Jami’an Tsaro Sun Ƙaddamar Da Aikin Ceto Limaman Da Aka Sace Bayan Taron APC A Zamfara 

September 14, 2026
Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Makiyaya Sun Yi Asarar Shanu 200,000 Ta Dalilin Rikice-Rikice – MACBAN

September 13, 2026
Gwamna lawal

Farashin Man Fetur Ya Sake Tashi A Abuja

September 13, 2026
Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

September 13, 2026
Gwamna lawal

Malamai Da Limamai 3,000 Sun Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Nasarar Tinubu A 2027

September 13, 2026
An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya

An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya

September 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.