ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Ƙasashen Musulmi Za Su Iya Kafa Ƙawancen Tsaro Don Tunkarar Abokan Gaba?

by Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
musulmi

Bayan harin da Isra’ila ta kai kan jagororin Hamas a Doha, babban birnin Ƙatar, akwai alamun cewa wani yunƙuri tsakanin ƙasashen Larabawa na kafa ƙungiyar tsaro mai kama da NATO na ƙara samun goyon baya.

Ƙasashen sun kira wani taro na ministocin harkokin waje a birnin na Doha ranar Lahadi, sannan a ranar Litinin shugabannin ƙasashen Larabawa, ciki har da na Iran Masoud Pezshkian da Firaiministan Iraƙ Muhammad Shia-al Sudani da kuma shugaban hukumar mulkin Falasɗinawa Mahmoud Abbas.

  • Shugabannin Larabawa Sun Amince Da Tsarin Gina Gaza Da Zai Lakume Dala Biliyan 53
  • Tinubu Ya Isa Kasar Saudiyya Domin Taron Hadin Kan Kasashen Larabawa Da Musulunci

Kuma a wannan lokaci shawarar da Masar ta bayar ta kafa dakarun haɗin gwiwa ta haifar da muhawara.

ADVERTISEMENT

Jaridar ‘The National’ ta ce Masar ta bayar da shawarar kafa wani ƙawancen tsaro mai kama da NATO, wanda za a riƙa karɓa-karɓar jagorancinsa tsakanin ƙasashen Larabawa 22, inda Masar ɗin za ta zama ta farko.

Kafar yaɗa labarai ta ‘The New Arab Media’ ta ce an fara bijiro da wannan shawara ce a shekara ta 2015 lokacin da yaƙin basasa ya ɓarke tsakanin dakarun Yemen da ƴ an tawayen Houthi, waɗanda suka karɓe iko da birnin Sanaa.

LABARAI MASU NASABA

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

A ɓangare ɗaya kuma Turkiyya na ƙara nuna damuwa bayan harin da Isra’ila ta kai a birnin Doha.

Mai magana da yawun ma’aikatar tsaro ta Turkiyya, Rear Admiral Zeki Akturk ya yi gargaɗin cewa “Isra’ila za ta iya faɗaɗa hare-harenta baya ga Ƙatar. Za ta iya ingiza yankin baki ɗaya cikin bala’i.”

Mece ce shawarar da Masar ta bayar?

Shawarar da Masar ta bayar ya ƙunshi samar da tsarin haɗe ayyukan sojin ƙasa da na sama da cibiyoyin tsaro, tare da haɗe cibiyoyin horaswa da ayyukan soji.

Haka nan kuma ƙasashen ne za su yanke hukunci kafin amfani da dakarun bayan tattaunawa a tsakaninsu.

Kafar yaɗa labarai ta Al Akhbar da ke Lebanon ta ce a ƙarƙashin tsarin, Masar ta ce za ta samar da dakaru 20,000, sannan Saudiyya za ta zamo ta biyu mafi bayar da gudumawa.

Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi ya tattauna da ƙasashe da dama a kan wannan batu, kuma akwai yiwuwar harin da Isra’ila ta kai a Doha zai iya farfaɗo da maganar.

An taɓa samun irin wannan ƙawance a lokuta daban-daban tsakanin ƙasashen yankin, kamar a lokacin yaƙin yankin Gulf da kuma yaƙe-yaƙen da aka yi a Isra’ila.

An taɓa ƙulla irin wannan ƙawancen tsaro a baya tsakanin ƙasashen Larabawa da na Musulmi wadda ake kira ‘Central Treaty Organisation’, wadda aka yi wa laƙabi da Yarjejeniyar Baghdad. Yarjejeniyar ta yi aiki daga shekara ta 1955 zuwa 1979.

Ƙasashen Larabawa sun yi mummunar suka kan harin da Isra’ila ta kai a Ƙatar

Firaiministan Iraƙi Mohammed Shia al-Sudani ya kuma yi kira da a samu ‘ƙawancen soji na ƙasashen Musulmai’.

Kafar yaɗa labarai ta Turkiyya, TRT World, ta ambato shi na cewa akwai buƙatar ɗaukar mataki na bai-ɗaya kan abubuwan da Isra’ila ta aikata a Gaza da kuma Ƙatar a baya-bayan nan.

Al-Sudani ya ce harin da Isra’ila ta kai a Doha, wanda ya kashe mambobin Hamas biyar da wani babban jami’in tsaron Ƙatar “taka dokokin duniya ne mai matuƙar mamaki” kuma tunatarwa ce kan cewa abubuwan da Isra’ila ke aikatawa barazana ce ga tsaron ɗaukacin yankin.

”Babu wani dalili da zai hana ƙasashen Musulmai haɗa kai domin samar da ƙawancen soji guda ɗaya domin kare kansu,” kamar yadda ya shaida wa tashar talabijin ta Al Jazeera, inda ya buƙaci ƙasashen Larabawa da na Musulmai su samar da haɗaka ta siyasa da tsaro da kuma tattalin arziki.

Ya kamata a hukunta Isra’ila – in ji Ƙatar

 “Lokaci ya yi da duniya za ta kawo ƙarshen baki biyu da ake yi sannan a hukunta Isra’ila kan laifukan da ta tafka,” in ji ministan harkokin waje na Ƙatar, gabanin taron da ƙasashen suka yi a ranar Litinin, kamar yadda sashen BBC Persia ya ruwaito.

Ya ce “Ya kamata Isra’ila ta sani cewa wannan yaƙi da take da ƴ an’uwanmu, Falasɗinawa, da nufin korar su daga ƙasarsu, ba zai yi nasara ba.”

Ƙatar ta yi martani da kakkausan harshe bayan harin da Isra’ila ta kai mata ranar 9 ga watan Satumba, kuma ta jaddada cewa yanzu a shirye take kan ko ma mene ne zai faru.

Ɗaya daga cikin manyan jami’an Hamas, Bassem Naim, ya ce ƙungiyar na fatan cewa za a samu “wani ƙwaƙƙwaran mataki na bai-ɗaya daga ƙasashen Larabawa da na Musulmai” kan Isra’ila.

Amurka na da sansanin sojin samanta mafi girma a faɗin Gabas ta tsakiya ne a Ƙatar. Baya ga haka, Ƙatar ta taka muhimmiyar rawa wajen tattaunawar sulhu tsakanin Amurka da Masar da kuma Isra’ila da Hamas.

Sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio wanda ya kai ziyara Isra’ila, ya nuna fushinsa kan harin da Isra’ila ta kai a Ƙatar, sai dai ya bayyana cewa wannan ba zai lalata kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin Amurka da Isra’ila ba.

Dama dai akwai ruɗani kan abin da mai magana da yawun fadar shugaban Amurka ta White House, Caroline Leɓitt ta ce game da bayanin da aka yi wa Ƙatar kan harin. Fadar White House ta ce ‘an sanar da Ƙatar kafin kai harin’, sai dai Firaiminstan Ƙatar ya ce ya ‘samu bayanin ne minti 10 bayan kai harin’.

Shin abu ne mai yiwuwa ƙasashen Larabawa su kafa ƙawance kamar NATO?

Batun kafa ƙawancen soji tsakanin ƙasashen Larabawa, mai kama da ƙawancen NATO, abu ne da ya daɗe, sai dai masana ba su da ƙwarin gwiwar cewa abu ne da zai yiwu.

Premanand Mishra, malami a cibiyar zaman lafiya da warware rikice-rikice ta Nelson Mandela a jami’ar Jamia Millia Islamia da ke Indiya, ya ce “An taɓa tattaunawa kan kafa ƙungiyar NATOn Larabawa, kuma Saudiyya ta bai wa batun muhimmanci sosai. Har ma an taɓa naɗa tsohon babban hafsan soji na Pakistan, Raheel Sharif a matsayin shugabanta, to amma sai batun ya gaza ci gaba.”

Ya ce “Muradun tsaro na dukkanin ƙasashen sun sha bamban ta yadda zai yi wahala a samu matsaya ɗaya a tsakaninsu.

Misali, Saudiyya da Iran za su iya watsi da bambance-bambancen da ke tsakaninsu? Domin idan har za a yi haɗakar soji, to akwai buƙatar yin musayar bayanan sirri.”

Duk da cewa akwai ƙoƙarin da aka yi a baya-bayan man na sulhuntawa tsakanin Saudiyya da Iran, babu tabbas kan ko an cimma wata matsaya mai ƙwari da za ta ita samar da ƙawance tsakanin ƙasashen yankin.

Premanand Mishra ya ce wannan shawara ta ƙawancen soji ta samo asali ne daga Masar, abin da ya rage shi ne a ga ko akwai ƙwaƙwarar aniyar aiwatarwa. Sannan kuma ko ƙasashen Yamma, musamman Amurka da ƙawancenta na NATO za su bari a aiwatar da shawarar”

Ya ce tabbas akwai batun kafa NATOn Larabawa a baya, kuma za a ci gaba da samun irin wannan batu a nan gaba, amma akwai shakku kan ko za a iya aiwatarwa.

Dr Mudassir Ƙamar, ƙaramin farfesa a Cibiyar nazarin yankin yammacin Asia a jami’ar Jawaharlal Nehru da ke birnin Delhi na Indiya, ya ce ƙasashen Larabawa na da ƙungiyoyi da dama da suka haɗu a ciki, kamar ƙungiyar Arab League, da OIC da kuma GCC.

Bayan haka akwai dakarun yaƙi da ta’addanci da ke ƙarƙashin jagorancin Saudiyya, to amma matsalar ita ce yadda za a warware matsalolin da ke tsakanin ƙasashen na Larabawa.

Mudassir Ƙamar ya ce “zai yi matuƙar wahala Isra’ila, wadda yanzu ba ta shiri da ƙasashen Larabawa da dama ta kawar da kai daga duk wani yunƙuri na samar da irin wannan ƙawance.”

musulmi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

MASU ALAKA

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato
Labarai

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno
Manyan Labarai

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna
Labarai

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Next Post
Gwamna Lawal Ya Raba Kayan Karatu 408,137 Ga Makarantun Gwamnatin Zamfara

Gwamna Lawal Ya Raba Kayan Karatu 408,137 Ga Makarantun Gwamnatin Zamfara

LABARAI MASU NASABA

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026
ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.