• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Sani Zai Kaddamar Da Cibiyar Kula Da Cutar Kansa Mai Gadaje 300 A Kaduna – Kwamishina

by Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
Gwamna Sani Zai Kaddamar Da Cibiyar Kula Da Cutar Kansa Mai Gadaje 300 A Kaduna – Kwamishina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Uba Sani ya yi alkawarin kammalawa tare da kaddamar da wani asibitin kwararru mai gadaje 300 wanda aka tanada musamman don kula da masu cutar kansa a Millennium city, da ke Kaduna a karshen shekarar 2024.

 

Wannan aikin asibitin wanda tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo ya kaddamar, ya samu tallafin dala miliyan 148 daga bankin cigaban Musulunci (IDB) da nufin samar da cikakkiyar cibiyar kiwon lafiya ga al’ummar jihar Kaduna.

  • Zaɓen Ƙananan Hukumomi: Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Yaƙin Neman Zaɓen APC
  • Sanatocin Arewa 12 Da Suka Gaza Gabatar Da Ƙudiri A Watanni 15

Duk da kokarin da gwamnatocin baya da suka hada da na Patrick Yakowa, Mukhtar Ramadan Yero, da Nasir Ahmed El-Rufai suka yi, har yanzu aikin bai kammala ba.

 

Labarai Masu Nasaba

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

Da take magana, kwamishiniyar lafiya ta jihar Hajia Umma K. Ahmed a wani taron manema labarai a ranar Laraba, da take bayyana irin nasarorin da gwamnatin Sanata uba Sani ta samu a fannin kiwon lafiya, ta ce, Gwamna Sani ya ce: “A cikin zango na karshe na shekarar 2024, zai gayyace ‘yan jarida domin kaddamar da kammala ginin wannan katafariyar cibiyar kiwon lafiya ta zamani.

 

“Kaddamar da wannan cibiya ta zamani, za ta kawo sauyi tare da gyara harkokin kiwon lafiya na Jiha tare da rage yawan fita zuwa kasashen ketare don neman magani, domin asibitin mai gadaje 300 yana da sashen binciken cututtukan daji da kuma magance cutar. ”

 

Gwamnan ya ce, tsaren-tsaren inganta kiwon lafiya ya bada fifiko matuka wajen samar da kayan aiki a dukkan matakan kiwon lafiya da suka hada da na farko, matsakaita da manya a jihar, inda ya ce, gwamnati na inganta manyan asibitoci 9, inda aka zabo uku-uku daga cikin shiyyoyi Uku da ke jihar.

 

“Asibitocin sun hada da Asibitin Maigana, Asibitin Rigasa, Asibitin Gwantu, Asibitin Ikara, Asibitin Patrick Ibrahim Yakowa, da Asibitin Giwa.”

 

Sauran sun hada da “Sabon Asibitin Tunawa da Dabo Lere, Asibitin Sabon Tasha, da Asibitin Kachia”. in ji ta.

 

Wadannan Asibitocin, a halin yanzu suna cikin matakai daban-daban na sake ginawa, sake fasali, da kuma samar da kayan aiki a matsayin wani bangare na shirin Gwamnati na inganta cibiyoyin kiwon lafiya.

 

Gwamnan ya kara da cewa, ana kokarin samar da ababen more rayuwa ne domin ganin an samu sauyi a kowane mataki domin samar da ingantacciyar kulawa ga al’ummar jihar Kaduna.

 

Hajiya Umma ta jaddada cewa: “Tun da ya hau kan karagar mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023, Gwamna Uba Sani ya nuna jajircewarsa na kawo sauyi a fannin kiwon lafiya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin Uba SaniKadunaKiwon Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kiyaye Halaltaccen Hakkin Falasdinawa

Next Post

Sin Ta Bukaci Kwamitin Sulhun MDD Da Ya Ingiza Sassauta Rikicin Lebanon Da Isra’ila

Related

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

2 hours ago
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

5 hours ago
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

5 hours ago
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

7 hours ago
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno
Labarai

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

9 hours ago
Labarai

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

12 hours ago
Next Post
Sin Ta Bukaci Kwamitin Sulhun MDD Da Ya Ingiza Sassauta Rikicin Lebanon Da Isra’ila

Sin Ta Bukaci Kwamitin Sulhun MDD Da Ya Ingiza Sassauta Rikicin Lebanon Da Isra’ila

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

September 6, 2025
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

September 6, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

September 6, 2025
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

September 6, 2025
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.