• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Ginin Kamfanin Haɗa Magunguna Na AMA-MED A Kaduna

bySulaiman
2 years ago
AMA-MED

Gwamna Uba Sani da shugabar kungiyar kasuwanci ta Duniya (WTO), Dakta Ngozi Okonjo Iweala, sun kaddamar da ginin katafaren kamfanin hada magunguna (AMA Medical Manufacturing Plant, Limited) ranar Alhamis, a Kudenda da ke, Kaduna.

Dakta Ngozi ta bayyana cewa, kamfanin an samar da shi ne don kasuwanci da zai habaka jihar Kaduna, Nijeriya da ma Nahiyar Afirka baki daya.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Mutane 61 A Wani Sabon Hari A Kaduna
  • Tallafin Da Amurka Ta Baiwa Gaza Wasan Kwaikwayo Ne

Tun da farko, Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, a yayin da ya ziyarci kamfanin AMA-MED, ya bayyana cewa, zuba jari a jihar abin a yaba ne kwarai da gaske kuma hakan zai taimaka matuka wajen yaba kokarin gwamnatin jihar Kaduna na bunkasa harkar lafiya.

Gwamnan ya kara da cewa, kamfamin zai taimaka matuka wajen samar da damammaki masu yawa ga al’ummar jihar na daga samar da ayyukan yi, habaka harkar kiwon lafiya da dai sauransu.

AMA-MED

LABARAI MASU NASABA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

Uba Sani ya nuna cewa, jihar Kaduna ce ta daya kan saukin gudanar da kasuwanci a fadin Nijeriya.

“Muna da tsarin kasuwanci mafi inganci a jihar Kaduna, don haka mutane da dama suke zuwa don zuba hannun jarinsu a jihar, kuma ba ni da shakka a raina tare da haɗin gwiwarmu da AMA-MED, za mu sake jawo hankalin wasu masu zuba jari da yawa zuwa jihar.

“Muna da su daga Dubai, Indiya, Indonesia, Morocco wadanda suke tare da mu a jihar kuma a shirye muke mu yi aiki tare da AMA-MED, ba ni da wata shakka a raina, AMA-MED za su zama mafi kyawu kuma babban kamfani a fannin masana’antar kiwon lafiya a duk fadin Nijeriya.

Bikin ya samu halartar wakilan gwamnati, sarakunan gargajiya, manyan ‘yan kasuwa, fitattun masana daga cikin gida da kasashen waje da daidai sauransu.

Daga cikinsu akwai, Wakiliyar Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima; Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani; mataimakiyar gwamna, Dr Hadiza; Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammad Ali Pate CON; Shugabar Kungiyar kasuwanci ta Duniya (WTO), Dakta Ngozi Okonjo Iweala; Sarkin Zazzau, Amb. Ahmed Nuhu Bamalli tare da wasu jami’an gwamnati.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
Next Post
Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version