• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Ginin Kamfanin Haɗa Magunguna Na AMA-MED A Kaduna

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Ginin Kamfanin Haɗa Magunguna Na AMA-MED A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Uba Sani da shugabar kungiyar kasuwanci ta Duniya (WTO), Dakta Ngozi Okonjo Iweala, sun kaddamar da ginin katafaren kamfanin hada magunguna (AMA Medical Manufacturing Plant, Limited) ranar Alhamis, a Kudenda da ke, Kaduna.

Dakta Ngozi ta bayyana cewa, kamfanin an samar da shi ne don kasuwanci da zai habaka jihar Kaduna, Nijeriya da ma Nahiyar Afirka baki daya.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Mutane 61 A Wani Sabon Hari A Kaduna
  • Tallafin Da Amurka Ta Baiwa Gaza Wasan Kwaikwayo Ne

Tun da farko, Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, a yayin da ya ziyarci kamfanin AMA-MED, ya bayyana cewa, zuba jari a jihar abin a yaba ne kwarai da gaske kuma hakan zai taimaka matuka wajen yaba kokarin gwamnatin jihar Kaduna na bunkasa harkar lafiya.

Gwamnan ya kara da cewa, kamfamin zai taimaka matuka wajen samar da damammaki masu yawa ga al’ummar jihar na daga samar da ayyukan yi, habaka harkar kiwon lafiya da dai sauransu.

AMA-MED

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Uba Sani ya nuna cewa, jihar Kaduna ce ta daya kan saukin gudanar da kasuwanci a fadin Nijeriya.

“Muna da tsarin kasuwanci mafi inganci a jihar Kaduna, don haka mutane da dama suke zuwa don zuba hannun jarinsu a jihar, kuma ba ni da shakka a raina tare da haɗin gwiwarmu da AMA-MED, za mu sake jawo hankalin wasu masu zuba jari da yawa zuwa jihar.

“Muna da su daga Dubai, Indiya, Indonesia, Morocco wadanda suke tare da mu a jihar kuma a shirye muke mu yi aiki tare da AMA-MED, ba ni da wata shakka a raina, AMA-MED za su zama mafi kyawu kuma babban kamfani a fannin masana’antar kiwon lafiya a duk fadin Nijeriya.

Bikin ya samu halartar wakilan gwamnati, sarakunan gargajiya, manyan ‘yan kasuwa, fitattun masana daga cikin gida da kasashen waje da daidai sauransu.

Daga cikinsu akwai, Wakiliyar Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima; Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani; mataimakiyar gwamna, Dr Hadiza; Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammad Ali Pate CON; Shugabar Kungiyar kasuwanci ta Duniya (WTO), Dakta Ngozi Okonjo Iweala; Sarkin Zazzau, Amb. Ahmed Nuhu Bamalli tare da wasu jami’an gwamnati.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AMA Medical Manufacturing LimitedJihar KadunaWTOZuba Jari
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

Related

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
Labarai

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

40 minutes ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

2 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

13 hours ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

14 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

15 hours ago
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
Labarai

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

18 hours ago
Next Post
Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.