ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutane 61 A Wani Sabon Hari A Kaduna

by Sadiq
2 years ago
Kaduna

Akalla mutane 61 ne wasu ‘yan bindiga suka sace a kauyen Buda da ke Karamar Hukumar Kajuru a Jihar Kaduna.

Wani mazaunin kauyen ya shaida wa manema labarai cewa ‘yan bindigar sun kai farmaki kauyen ne da misalin karfe 11:45 na daren ranar Litinin, inda suka yi ta harbe-harbe kafin su tafi da wadanda abin ya shafa.

  • SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 2
  • Sin Ba Ta Amince Amurka Ta Samarwa Yankin Taiwan Makamai Ba

Mazaunin kauyen wanda ya bayyana sunansa da Dauda Kajuru, ya ce maharan sun yi wa mutanen kawanya kafin daga bisani su sace da dama daga cikinsu.

ADVERTISEMENT

“Abin da ya faru jiya (Litinin) abin ban tsoro ne. ‘Yan bindigar sun zo ne da nufin sace mutane da dama wanda zai zarce na daliban makaranta a kauyen Kuriga da ke Karamar Hukumar Chikun, amma saurin kawo dauki da sojoji suka yi daga Kajuru, ya taimaka wajen rage adadin wadanda suka sace.

“Yan uwana na cikin wadanda aka sace jiya kuma babu bayanan da muka samu har zuwa safiyar yau,” in ji Manyu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ya koka kan yadda aka sauya wani Kwamandan sojoji da aka fi sani da (Tega), wanda ke kokari wajen dakile hare-haren ta’addancin a kauyen.

“Zan fada muku cewa lokacin da Kwamanda Tega yake wajen, hare-haresu ya yi baya, kuma mutum na iya harkokinsa babu fargabar sace shi saboda ya san yanayinsu da kuma yanayin ayyukansu.

“Abin takaici ne dauke Kwamanda Tega daga Karamar Hukumar Kajuru yayin da zaman lafiya ya fara dawowa a kauyukanmu,” in ji shi.

Wani mazaunin yankin mai suna Lawal Abdullahi wanda ya tsallake rijiya da baya amma matarsa na cikin wadanda aka sace, ya tabbatar da sace mutane 61.

Ya ce akwai maza da mata da yara da kuma wata mata mai shayarwa.

“Al’amarin ya tayar min da hankali domin ba mu ji duriyarsu ba tun bayan faruwar lamarin a ranar Litinin.

“Muna kira ga gwamnati da ta dauki mataki kuma ta tabbatar da cewa iyalanmu sun dawo cikin gaggawa,” in ji shi.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, ASP Mansur Hassan ba amsa kiran wayar da aka masa ba, yayin da gwamnatin jihar kuma ba ce komai game da lamarin ba.

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 20 A Matsayin Kudin Fansar Almajirai 15 Da Suka Sace A Sakkwato

'Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 20 A Matsayin Kudin Fansar Almajirai 15 Da Suka Sace A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.