ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutane 61 A Wani Sabon Hari A Kaduna

by Sadiq
2 years ago
Kaduna

Akalla mutane 61 ne wasu ‘yan bindiga suka sace a kauyen Buda da ke Karamar Hukumar Kajuru a Jihar Kaduna.

Wani mazaunin kauyen ya shaida wa manema labarai cewa ‘yan bindigar sun kai farmaki kauyen ne da misalin karfe 11:45 na daren ranar Litinin, inda suka yi ta harbe-harbe kafin su tafi da wadanda abin ya shafa.

  • SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 2
  • Sin Ba Ta Amince Amurka Ta Samarwa Yankin Taiwan Makamai Ba

Mazaunin kauyen wanda ya bayyana sunansa da Dauda Kajuru, ya ce maharan sun yi wa mutanen kawanya kafin daga bisani su sace da dama daga cikinsu.

ADVERTISEMENT

“Abin da ya faru jiya (Litinin) abin ban tsoro ne. ‘Yan bindigar sun zo ne da nufin sace mutane da dama wanda zai zarce na daliban makaranta a kauyen Kuriga da ke Karamar Hukumar Chikun, amma saurin kawo dauki da sojoji suka yi daga Kajuru, ya taimaka wajen rage adadin wadanda suka sace.

“Yan uwana na cikin wadanda aka sace jiya kuma babu bayanan da muka samu har zuwa safiyar yau,” in ji Manyu.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Ya koka kan yadda aka sauya wani Kwamandan sojoji da aka fi sani da (Tega), wanda ke kokari wajen dakile hare-haren ta’addancin a kauyen.

“Zan fada muku cewa lokacin da Kwamanda Tega yake wajen, hare-haresu ya yi baya, kuma mutum na iya harkokinsa babu fargabar sace shi saboda ya san yanayinsu da kuma yanayin ayyukansu.

“Abin takaici ne dauke Kwamanda Tega daga Karamar Hukumar Kajuru yayin da zaman lafiya ya fara dawowa a kauyukanmu,” in ji shi.

Wani mazaunin yankin mai suna Lawal Abdullahi wanda ya tsallake rijiya da baya amma matarsa na cikin wadanda aka sace, ya tabbatar da sace mutane 61.

Ya ce akwai maza da mata da yara da kuma wata mata mai shayarwa.

“Al’amarin ya tayar min da hankali domin ba mu ji duriyarsu ba tun bayan faruwar lamarin a ranar Litinin.

“Muna kira ga gwamnati da ta dauki mataki kuma ta tabbatar da cewa iyalanmu sun dawo cikin gaggawa,” in ji shi.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, ASP Mansur Hassan ba amsa kiran wayar da aka masa ba, yayin da gwamnatin jihar kuma ba ce komai game da lamarin ba.

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 20 A Matsayin Kudin Fansar Almajirai 15 Da Suka Sace A Sakkwato

'Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 20 A Matsayin Kudin Fansar Almajirai 15 Da Suka Sace A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.