ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutane 61 A Wani Sabon Hari A Kaduna

by Sadiq
2 years ago
Kaduna

Akalla mutane 61 ne wasu ‘yan bindiga suka sace a kauyen Buda da ke Karamar Hukumar Kajuru a Jihar Kaduna.

Wani mazaunin kauyen ya shaida wa manema labarai cewa ‘yan bindigar sun kai farmaki kauyen ne da misalin karfe 11:45 na daren ranar Litinin, inda suka yi ta harbe-harbe kafin su tafi da wadanda abin ya shafa.

  • SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 2
  • Sin Ba Ta Amince Amurka Ta Samarwa Yankin Taiwan Makamai Ba

Mazaunin kauyen wanda ya bayyana sunansa da Dauda Kajuru, ya ce maharan sun yi wa mutanen kawanya kafin daga bisani su sace da dama daga cikinsu.

ADVERTISEMENT

“Abin da ya faru jiya (Litinin) abin ban tsoro ne. ‘Yan bindigar sun zo ne da nufin sace mutane da dama wanda zai zarce na daliban makaranta a kauyen Kuriga da ke Karamar Hukumar Chikun, amma saurin kawo dauki da sojoji suka yi daga Kajuru, ya taimaka wajen rage adadin wadanda suka sace.

“Yan uwana na cikin wadanda aka sace jiya kuma babu bayanan da muka samu har zuwa safiyar yau,” in ji Manyu.

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Ya koka kan yadda aka sauya wani Kwamandan sojoji da aka fi sani da (Tega), wanda ke kokari wajen dakile hare-haren ta’addancin a kauyen.

“Zan fada muku cewa lokacin da Kwamanda Tega yake wajen, hare-haresu ya yi baya, kuma mutum na iya harkokinsa babu fargabar sace shi saboda ya san yanayinsu da kuma yanayin ayyukansu.

“Abin takaici ne dauke Kwamanda Tega daga Karamar Hukumar Kajuru yayin da zaman lafiya ya fara dawowa a kauyukanmu,” in ji shi.

Wani mazaunin yankin mai suna Lawal Abdullahi wanda ya tsallake rijiya da baya amma matarsa na cikin wadanda aka sace, ya tabbatar da sace mutane 61.

Ya ce akwai maza da mata da yara da kuma wata mata mai shayarwa.

“Al’amarin ya tayar min da hankali domin ba mu ji duriyarsu ba tun bayan faruwar lamarin a ranar Litinin.

“Muna kira ga gwamnati da ta dauki mataki kuma ta tabbatar da cewa iyalanmu sun dawo cikin gaggawa,” in ji shi.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, ASP Mansur Hassan ba amsa kiran wayar da aka masa ba, yayin da gwamnatin jihar kuma ba ce komai game da lamarin ba.

MASU ALAKA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 20 A Matsayin Kudin Fansar Almajirai 15 Da Suka Sace A Sakkwato

'Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 20 A Matsayin Kudin Fansar Almajirai 15 Da Suka Sace A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.