ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Ginin Kamfanin Haɗa Magunguna Na AMA-MED A Kaduna

by Sulaiman
2 years ago
AMA-MED

Gwamna Uba Sani da shugabar kungiyar kasuwanci ta Duniya (WTO), Dakta Ngozi Okonjo Iweala, sun kaddamar da ginin katafaren kamfanin hada magunguna (AMA Medical Manufacturing Plant, Limited) ranar Alhamis, a Kudenda da ke, Kaduna.

Dakta Ngozi ta bayyana cewa, kamfanin an samar da shi ne don kasuwanci da zai habaka jihar Kaduna, Nijeriya da ma Nahiyar Afirka baki daya.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Mutane 61 A Wani Sabon Hari A Kaduna
  • Tallafin Da Amurka Ta Baiwa Gaza Wasan Kwaikwayo Ne

Tun da farko, Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, a yayin da ya ziyarci kamfanin AMA-MED, ya bayyana cewa, zuba jari a jihar abin a yaba ne kwarai da gaske kuma hakan zai taimaka matuka wajen yaba kokarin gwamnatin jihar Kaduna na bunkasa harkar lafiya.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya kara da cewa, kamfamin zai taimaka matuka wajen samar da damammaki masu yawa ga al’ummar jihar na daga samar da ayyukan yi, habaka harkar kiwon lafiya da dai sauransu.

AMA-MED

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Uba Sani ya nuna cewa, jihar Kaduna ce ta daya kan saukin gudanar da kasuwanci a fadin Nijeriya.

“Muna da tsarin kasuwanci mafi inganci a jihar Kaduna, don haka mutane da dama suke zuwa don zuba hannun jarinsu a jihar, kuma ba ni da shakka a raina tare da haɗin gwiwarmu da AMA-MED, za mu sake jawo hankalin wasu masu zuba jari da yawa zuwa jihar.

“Muna da su daga Dubai, Indiya, Indonesia, Morocco wadanda suke tare da mu a jihar kuma a shirye muke mu yi aiki tare da AMA-MED, ba ni da wata shakka a raina, AMA-MED za su zama mafi kyawu kuma babban kamfani a fannin masana’antar kiwon lafiya a duk fadin Nijeriya.

Bikin ya samu halartar wakilan gwamnati, sarakunan gargajiya, manyan ‘yan kasuwa, fitattun masana daga cikin gida da kasashen waje da daidai sauransu.

Daga cikinsu akwai, Wakiliyar Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima; Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani; mataimakiyar gwamna, Dr Hadiza; Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammad Ali Pate CON; Shugabar Kungiyar kasuwanci ta Duniya (WTO), Dakta Ngozi Okonjo Iweala; Sarkin Zazzau, Amb. Ahmed Nuhu Bamalli tare da wasu jami’an gwamnati.

AMA-MED
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.