• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Dauki Sabbin Ma’aikata 1,683

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad ya fara wa’adin mulkinsa na biyu da daukar sabbin ma’aikata 1,684 a bangarori daban-daban na aikin gwamnati.

Hakan na kunshe ne cikin manufar shawo kan karancin ma’aikatan da ake fuskanta a wasu ma’aikatu, fannoni da rassan gwamnati.

  • Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Nada Masu Bashi Shawara 20
  • Kotu Ta Dakatar Da EFCC, ICPC, DSS Daga Tsare Sanata Yari

Da yake zantawa da ‘yan jarida kan wannan lamarin, shugaban ma’aikatan jihar Bauchi, Alhaji Yahuza Adamu Haruna, ya shaida cewar, daga cikin ma’aikatan, sama da mutum dubu daya an dauke su ne a bangaren koyar da ilimi domin shawo kan matsalar da ake fuskanta a harkar ilimi a jihar.

Ya ce, malaman da aka dauka sun kunshi har da masu kuyar da muhimman darussa da suka hada da na turanci, lissafi, biology, Biology, Chemistry, Physics da kuma na ICT. Dukka a bangaren ilimin, ya kuma sanar da cewa, gwamnan ya kuma amince da daukan wasu karin malamai guda 154 da za su yi aiki a kwalejin koyar da ilimi ta Aminu Saleh da ke Azare.

Idan za ku tuna dai, a jawabinsa na shan rantsuwar kama aiki a matsayin gwamnan jihar Bauchi karo na biyu, Bala Muhammad ya shaida cewar, jihar ta cire takunkumin daukan ma’aikata domin bai wa matasan da suka dace cikakken damar shigowa a dama da su wajen tafiyar da aikin gwamnati, kan hakan ne ya nuna cewa kwanan nan za a fara daukan sabbin ma’aikata.

LABARAI MASU NASABA

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

Yahuza ya ce, gwamnati mai ci a jihar ta Bala Muhammad ta himmatu wajen tabbatar da aiki mai inganci domin kyautata rayuwar al’umma da cigaban Jihar Bauchi.

Ya ce, “Sannu a hankali gwamna Bala Muhammad ya amince da fara daukan ma’aikata, inda ya amince da daukan ma’aikata dubu daya a ma’aikatar ilimi sannan ya amince da daukan wasu ma’aikatan a fannoni daban-daban.

“A bangaren harkar noma ma, gwamnan ya amince da daukan ma’aikatan domin magance matsalar da ake fama da shi na karancin malaman gona.”

“Tun lokacin da gwamnan ya yi alkawari a wajen jawabinsa na rantsuwa, ga shi ba da jimawa ba har ya amince da daukan ma’aikatan, kuma nan ba da jimawa ba ma zai sake daukan wasu. Wannan abun yabawa ne matuka da masa jinjina.”

Daga nan sai ya gargadi masu bukatar aiki da cewa su sanya lura kada wani ko wasu su zo musu da cewa su basu wani abu domin samar musu da aikin yi, “Don Allah a taimakemu duk wanda ya ce a ba shi sisi don ya samar ma wani da aikin yi, to a yi gaggawar zuwa domin samar mana, mu kuma za mu dauki mataki kan kowaye,” ya shaida.

Shugaban ma’aikatan ya bada jerin sabbin ma’aikatan da gwamnan ya dauka da cewa ma’aikatar ilimi ta samu sabbin ma’aikata 1,000; ma’aikatar aikin gona 44; ma’aikatar bunkasa aikin gona (BSADP) 206; ma’aikatar samar da kayan noma da rarrabashi (BASADA) ta samu sabbin jami’ai 90; sai ma’aikatar mata da cigaban yara mai sabbin ma’aikata 70; kwalejin ilimi ta Aminu Saleh, Azare 154; sai kuma kotun daukaka kara ta Shari’a mai sabbin ma’aikata 120.

Daga bisani ya nemi sabbun ma’aikatan da su hada kai da gwamnatin jihar domin ciyar da aiki da jihar Bauchi gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato
Labarai

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
Next Post
Qin Gang Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministan Harkokin Wajen Afirka Ta Kudu

Qin Gang Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministan Harkokin Wajen Afirka Ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

November 7, 2025
Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.