• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Ƙara Mafi Ƙarancin Albashi Daga N7,000 Zuwa N30,000, Za A Fara Biya Daga Yuni

by Leadership Hausa
12 months ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Ƙara Mafi Ƙarancin Albashi Daga N7,000 Zuwa N30,000, Za A Fara Biya Daga Yuni
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya bayyana cewa gwamnatin sa za ta fara biyan mafi ƙarancin albashi na Naira Dubu Talatin a wata mai zuwa na Yuni.

Gwamnan ya yi wannan albashir ɗin ne a ranar Larabar nan a Lokacin da ya ke ganawa da shugabannin ƙungiyar ƙwadago ta jihar Zamfara.

A cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris ya fitar yau a Gusau, ya bayyana cewa aiwatar da wannan mafi ƙarancin albashi ya nuna azamar gwamnatin jihar ne na kyautata jin daɗin ma’aikatan.

Sanarwar ta Idris ta ci gaba da ƙarin haske da cewa, gwamnatin jihar Zamfara za ta fara biyan mafi ƙarancin albashi na Naira Dubu 30, maimakon Naira 7,000 da suke karɓa, za a fara biya daga watan Yunin nan mai zuwa.

A lokacin da ya ke ganawa da shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago ta NLC da na Malamai ta TUC, Gwamna Lawal ya bayyana cewa fara biyan wannan mafi ƙarancin albashi na Naira Dubu 30, wani yunƙuri ne na ƙara wa ma’aikatan Zamfara azama.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

zamfara

“A yau, ina so in sanar da shugabannin ƙungiyar ƙwadago ta jihar Zamfara cewa gwamnati na za ta fara biyan mafi ƙarancin albashi na Naira dubu 30 a watan Yuni.

“Tun lokacin da na hau kujerar gwamnan jihar Zamfara, gwamnati na ta aiwatar da sauye-sauye da dama na jin daɗin ma’aikatan gwamnati domin tabbatar da walwalar su.

“Mun samu nasarar biyan albashin ma’aikata na watanni uku da aka riƙe, biyan kuɗin hutu da sauran alawus-alawus.

“Gwamnati na ta biya jimillar Naira Biliyan 4,337,087,490 a rukuni huɗu ga waɗanda suka yi ritaya daga matakin jiha da ƙananan hukumomi, waɗanda ba a biya su haƙƙoƙin su ba tun shekarar 2011.

“Muna da wasu tsare-tsare na inganta ayyukan ma’aikatan gwamnati a Zamfara. Babu wani ma’aikaci da zai yi fargabar yin ritaya, saboda za mu tabbatar da biyan kuɗin ritaya a kan kari ba tare da wani jinkiri ba. Mun himmatu wajen aikin jin daɗin al’umma.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlbashiGwamnatin jihar ZamfaraƘwadagoMa'aikataZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Za A Yi Gagarumin Bikin Cikar Gwamnatin Tinubu Shekara Ɗaya Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai

Next Post

Sin Ta Nanata Wajibcin Kiyaye Fararen Hula Ta Hanyar Kawo Karshen Rikici

Related

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

1 hour ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

2 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

3 hours ago
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

4 hours ago
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata
Labarai

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

6 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

8 hours ago
Next Post
Sin Ta Nanata Wajibcin Kiyaye Fararen Hula Ta Hanyar Kawo Karshen Rikici

Sin Ta Nanata Wajibcin Kiyaye Fararen Hula Ta Hanyar Kawo Karshen Rikici

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.