• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Ƙara Mafi Ƙarancin Albashi Daga N7,000 Zuwa N30,000, Za A Fara Biya Daga Yuni

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Ƙara Mafi Ƙarancin Albashi Daga N7,000 Zuwa N30,000, Za A Fara Biya Daga Yuni
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya bayyana cewa gwamnatin sa za ta fara biyan mafi ƙarancin albashi na Naira Dubu Talatin a wata mai zuwa na Yuni.

Gwamnan ya yi wannan albashir ɗin ne a ranar Larabar nan a Lokacin da ya ke ganawa da shugabannin ƙungiyar ƙwadago ta jihar Zamfara.

A cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris ya fitar yau a Gusau, ya bayyana cewa aiwatar da wannan mafi ƙarancin albashi ya nuna azamar gwamnatin jihar ne na kyautata jin daɗin ma’aikatan.

Sanarwar ta Idris ta ci gaba da ƙarin haske da cewa, gwamnatin jihar Zamfara za ta fara biyan mafi ƙarancin albashi na Naira Dubu 30, maimakon Naira 7,000 da suke karɓa, za a fara biya daga watan Yunin nan mai zuwa.

A lokacin da ya ke ganawa da shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago ta NLC da na Malamai ta TUC, Gwamna Lawal ya bayyana cewa fara biyan wannan mafi ƙarancin albashi na Naira Dubu 30, wani yunƙuri ne na ƙara wa ma’aikatan Zamfara azama.

Labarai Masu Nasaba

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

zamfara

“A yau, ina so in sanar da shugabannin ƙungiyar ƙwadago ta jihar Zamfara cewa gwamnati na za ta fara biyan mafi ƙarancin albashi na Naira dubu 30 a watan Yuni.

“Tun lokacin da na hau kujerar gwamnan jihar Zamfara, gwamnati na ta aiwatar da sauye-sauye da dama na jin daɗin ma’aikatan gwamnati domin tabbatar da walwalar su.

“Mun samu nasarar biyan albashin ma’aikata na watanni uku da aka riƙe, biyan kuɗin hutu da sauran alawus-alawus.

“Gwamnati na ta biya jimillar Naira Biliyan 4,337,087,490 a rukuni huɗu ga waɗanda suka yi ritaya daga matakin jiha da ƙananan hukumomi, waɗanda ba a biya su haƙƙoƙin su ba tun shekarar 2011.

“Muna da wasu tsare-tsare na inganta ayyukan ma’aikatan gwamnati a Zamfara. Babu wani ma’aikaci da zai yi fargabar yin ritaya, saboda za mu tabbatar da biyan kuɗin ritaya a kan kari ba tare da wani jinkiri ba. Mun himmatu wajen aikin jin daɗin al’umma.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlbashiGwamnatin jihar ZamfaraƘwadagoMa'aikataZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Za A Yi Gagarumin Bikin Cikar Gwamnatin Tinubu Shekara Ɗaya Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai

Next Post

Sin Ta Nanata Wajibcin Kiyaye Fararen Hula Ta Hanyar Kawo Karshen Rikici

Related

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

2 hours ago
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

11 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

12 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

12 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

13 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

15 hours ago
Next Post
Sin Ta Nanata Wajibcin Kiyaye Fararen Hula Ta Hanyar Kawo Karshen Rikici

Sin Ta Nanata Wajibcin Kiyaye Fararen Hula Ta Hanyar Kawo Karshen Rikici

LABARAI MASU NASABA

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.