ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Ayyukan Gina Cibiyoyin Masan’antu Da Gina Asibitin A Kauran Namoda

by Hussein Yero
2 years ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya kaddamar da ayyukan gina cibiya koyon sana’oi uku a Karamar Hukumar Kauran Namoda.

Babban mataimaki na musamman na gwamna Dauda Lawal ne, Suleman Bala Idris, ya bayyana haka a takardar da ya sanya wa hannun ga manema labarai.

  • Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 4 Na Binciken Yanayi Samfurin Tianmu-1
  • Bashin Amurka Ya Kai Sabon Matsayi Wanda Ke Barazana Ga Tattalin Arzikin Kasar

A cewarsa, an shirya gina cibiyoyin koyar da sana’o’i guda uku a shiyyoyin Sanatoci uku na Jihar Zamfara.

ADVERTISEMENT

Wadannan cibiyoyi za su kasance kamar haka a karamar hukumar Gusau na shiyyar Zamfara ta Tsakiya, da karamar hukumar Kauran Namoda ta Arewa, da kuma karamar hukumar Gummi ta shiyyar Zamfara ta Yamma.

Ya ce: “A jiya Gwamna Dauda Lawal ya dauki wani muhimmin mataki na cika alkawuran yakin neman zabe ta hanyar kaddamar da muhimman ayyukan more rayuwa a karamar hukumar Kauran Namoda.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

“Gwamnan ya kaddamar da sana’o’i da cibiyar koyar da sana’o’i a Kwalejin Fasaha ta Gwamnati da ke Kauran Namoda. Cibiyar tana da ajujuwa shida, dakin gwaje-gwaje, bita biyu, dakin kwamfuta da ofisoshin ma’aikata.

“A yayin kaddamar da aikin, Gwamna Lawal ya jaddada cewa ilimi na daga cikin manyan abubuwan da gwamnatin Zamfara ta sa gaba, kuma masu ruwa da tsaki suna aiki tare domin ganin an yi wa tsarin karatun jihar garambawul.”

Sauran ayyukan da Gwamna Dauda Lawal ya kaddamar a karamar hukumar sun hada da gina cibiyar ci gaban mata, da makarantun tsangaya, da kuma sake gina babban asibitin Kauran Namoda da gyara shi.

“Cibiyar ci gaban mata za ta kasance cibiyar karfafa mata a mazabar majalisar dattawa. Cibiyar za ta kasance da kayan aiki na zamani don cikakken aiki.

“Gwamna Dauda Lawal ya aza harsashin ginin babban asibitin Kauran Namoda da kuma gyara shi. Ya yi alkawarin samar da kwararrun likitoci da ma’aikatan jinya tare da jaddada kudirinsa na samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya a fadin jihar.

“Kwamitin makarantar Islamiyya ta Tsangaya, Gwamna Dauda Lawal ya sanar da cewa gwamnatin Jihar Zamfara za ta gina irin wadannan makarantu a dukkanin shiyyoyin Sanatoci uku na jihar. Wannan shiri na da nufin sabunta tsarin makarantar Islamiyya ta Tsangaya da samar da damammaki ga daliban”.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule
Manyan Labarai

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna
Labarai

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Next Post
An Ceto Mutum 3 Bayan Musayar Wuta Da ‘Yan Bindiga A Jihar Kwara

An Ceto Matafiya 21 A Kogi Sa'o'i 48 Bayan Sace Su

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.