• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Sauke Nauyin Bashin Haƙƙoƙin Ma’aikata Na Fiye Da Naira Biliyan 4

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Sauke Nauyin Bashin Haƙƙoƙin Ma’aikata Na Fiye Da Naira Biliyan 4
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal ya biya tsofaffin ma’aikatan jihar bashin haƙƙoƙin su na barin aiki, wato Garatuti, wanda suka biyo tun na shekarar 2011, kuɗaɗen da suka haura Naira Biliyan 4.

Ma’aikatan jiha da na Ƙananan Hukumomin jihar da su ka bar aiki, ba su samu haƙƙoƙin su ba na tsawon waɗannan shekaru, an tantance su an biya su.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa an biya tsofaffin ma’aikatan jihar da na Ƙananan Hukumomi waɗannan kuɗaɗe bayan tantance sahihancin su.

Ya ce, gwamnatin jihar Zamfara ta biya tsabar kuɗin da ya kai ma Naira Biliyan 4,337,087,492.06 a rukunoni huɗu na tsofaffi ma’aikatan.

Sanarwar ta Sulaiman Bala ta ce, “A watan Faburairu, Gwamna Dauda Lawal ya kafa wani Kwamiti, wanda aka ɗora ma alhakin tantancewa tare da biyan tsofaffin ma’aikatan da suka bar aiki tun shekarar 2011, a ƙoƙarin sa na gyara tsarin aikin gwamnati a jihar Zamfara.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

  • Sabon Shirin Auren Zawarawan Kano A Sikeli

 

“Bayan kammala wannan tantancewar, sai ta bayyanar wa gwamnati cewa ana bin jiha da Ƙananan Hukumomi Naira Biyan 13.4.

“A biyan rukuni na farko, na biyu da na uku, an biya mutum 1,088 da aka tantance dukkan haƙƙoƙin su, inda aka biya N1,836,836,018.95

“A wannan watan, an biya mutum 284 da aka tantance kuɗaɗen su, wanda ya kai ma N499,435,942.42 a rukuni na huɗu. Hukumar Fansho ta jiha ta biya kuɗaɗen da suka kai ma N2,336,271,961.37.

“Bugu da ƙari, akwai ma’aikatan Ƙananan Hukumomi da Malaman Firamare su kimanin 1,744, waɗanda suka bar aiki a tsakanin shekarun 2011 da 2018, kuma tuni an biya su haƙƙoƙin su da ya kai ma Naira Biliyan N2,000,815,530.69 a rukuni huɗu.

“Wannan biyan bashin kuɗin barin aiki, ba ƙaramin gagarumin ci gaba ba ne a wannan gwamnatin, wanda kuma babu makawa, zai kawo sauƙi ga rayuwar waɗanda suka amfana, bayan jiran tsammani na shekaru masu yawa.

“Gwamnatin Dauda Lawal ta nuna aniyar ta na jajircewa wajen cika alƙawuran da ta yi wa al’ummar jihar Zamfara.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BashiDauda LawalGwamnaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

APC Ba Komai Ba Ce Illa Barin Jikin PDP Da Ya Rube – Sule Lamido

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Manoma 30 Da Wani Malami A Zamfara

Related

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

11 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

11 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

13 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

16 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

16 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

17 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Manoma 30 Da Wani Malami A Zamfara

'Yan Bindiga Sun Kashe Manoma 30 Da Wani Malami A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.