Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Gwamnati Za Ta Bunƙasa Harkar Wasanni A Kebbi

by Tayo Adelaja
October 3, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Umar Faruk, Birnin-Kebbi

Gwamnan Abubakar Atiku Bagudu na Jihar Kebbi ya  bayyana yunƙurin gwamnatinsa kan bunƙasa harakar wasannin a jihar.

Gwamnan ya bayyana hakan ne kwanan nan a Birnin-Kebbi yayin da yake jawabi  a wurin taron bikin bada kyautar wasannin guje-guje da ma’aikatar ilimi ta Jihar Kebbi ta shirya  ga makarantun yankunan ilimi guda biyar na cikin jihar a ƙarƙashin jagoranci kwamishinan ilimi na jihar, Alhaji Muhammad Magawata Aliero.

Har ila yau, ya ce wannan tsarin da ma’aikatar ilimi ta Jihar Kebbi ta fito da shi wata hanya ce ta ƙara farfaɗo da harakar wasannin a jihar a tsakanin makarantun sakandare a duk faɗin jihar, tare da cewa yin hakan zai ƙara ɗaga  martaba  da darajar jihar kan harakar wasanni. Ya ci gaba da cewa jihar za ta shiga  gasar guje-gujen da Jihar Legas ta shirya wanda  za a gudanar nan ba da jimawa ba. Saboda haka ya ce, wannan shiri na ma’aikatar ilimi zai taimaka ainun ga shiga gasar Jihar Legas.

Yankunan da suka fafata a gasar sun haɗa da yankin Birnin-Kebbi, Yakin Bunza, Yankin Zuru, Yankin Yauri, Yankin Argungu da kuma Yankin Jega. Inda  aka gudanar da guje-guje na mita 400 da mita 800 da mita 100 da kuma  mita 1500 a tsakanin maza da mata.

Bayan kammala gasar, a gudun mita 400 na mata yankin Birnin-Kebbi ya zo na ɗaya,  sai  yankin Zuru na biyu da kuma yankin Bunza a matsayin na uku. Sannan

a gudun mita 400 na maza, yankin Argungu ya ciri tuta a matsayin na ɗaya, sai yankin Jega na biyu da kuma yankin Zuru a matsayin na uku.

A gudun mita 1500 na mata, yankin Birnin-Kebbi shi ne ya zo na ɗaya, sai yankin Zuru na biyu da kuma Yauri a matsayin na uku. A mita 1500 na maza kuwa, yankin Bunza ya yi na ɗaya, sai yankin Birnin-Kebbi na biyu da kuma yankin Zuru na uku. A gudun mita 800 kuwa, ɓangare maza yankin Argungu na ɗaya, yankin Jega na biyu, sanna yankin Bunza na uku.

A ƙarshe, Gwamnan Bagudu ya wasu kyaututtuka ga ‘yan wasan da suka yi nasara, haka shi ma kwamishinan kuɗi na jihar Alhaji Muhammad Ibrahim Augie, da mataimakin gwamnan jihar Samaila Yombe Dabai, sakataren gwamnatin jihar Alhaji Babale Umar Yauri , shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kebbi Barista  Attahiru Maccido da kuma tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sanata Saminu Turaki.

A nasa jawabin, kwamishinan ilimi na jihar Alhaji Muhammad Magawata Aliero, ya yi godiya ga Gwamna Bagudu kan irin  goyon bayan da yake bai wa ma’aikatar ilimi kan bunƙasa harakar ilimi a jihar da kuma muhinmanci da yake nuna wa kan harakar wasannin makarantun sakandare da kuma sauran muƙarraban gwamnatin jihar da ma’aikatan ma’aikatar ilimi da suka bada tasu gudunmawa waje tabbatar da wannan gasa gudana cikin nasara.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Za Ta Horar Da Matasa 300 Sana’o’i A Bauchi

Next Post

An Yi Wa ‘Yan Jarida Bita Kan Harkokin Bankin Musulunci A Kano

RelatedPosts

Garkuwa

An Kama Sojan Da Ke Kai Wa ‘Yan Ta’adda Kayan Sojoji A Zamfara

by Sulaiman Ibrahim
8 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim "An kama wani jami’in soja da budurwarsa...

Aikin Wutar Mambilla  A Takardu Kawai Yake, Inji Gwamnonin Arewa Maso Gabas

Aikin Wutar Mambilla A Takardu Kawai Yake, Inji Gwamnonin Arewa Maso Gabas

by Sulaiman Ibrahim
11 hours ago
0

Kungiyar gwamnonin arewa maso gabas sun nuna rashin jin dadin...

Bindiga

Gwamna Ortom Ya Yabawa Umarnin Buhari Na Hana Mallakar  AK47 Ba Bisa Ka’ida Ba

by Muhammad
12 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Gwamnan Jihar Benue Samuel Ortom a ranar...

Next Post

An Yi Wa ‘Yan Jarida Bita Kan Harkokin Bankin Musulunci A Kano

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version