• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Buhari Za Ta Bar Wa Tinubu Bashin Naira Tiriliyan 46.25

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, zai bar wa gwamnati mai zuwa nauyin bashin da ya kai har na Naira tiriliyan 46.25.

Ofishin da ke kula ba bibiyar bashin kasar nan DMO ya bayyana cewa, jimlar bashin da ake bin Nijeriya, ya kai yawan Naira tiriliyan 46.25.

  • An Bude Dandalin Zuba Jari Tsakanin Kasashen Sin Da Nijar A Yamai

Kafar yada labarai ta Daily Post ta ruwaito cewa, duk da kurara da yawan dimbin bashin ya janyo, gwamnatin tarayya ta sanar da cewa, ta samu karin amincewar ciwo wani bashin daga gun babban bankin duniya wanda ya kai Naira biliyan 369 kafin a cire tallafin man fetur a watan Juni na 2023.

A cikin shekaru takwas na gwamnatin Buhari, bashin da ake bin Nijeriya ya karu daga Naira tiriliya 12.6 a 2015 zuwa sama da Naira 46 tiriliyan a 2023.

Lamarin ya ci gaba da haifar da damuwa, musamman ganin cewa, Asusun bayar da lamuni IMF ya shelanta cewa, Nijeriya har ta kai matsayin taste Asusun ta wajen biyan bashi a 2022.

Labarai Masu Nasaba

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Hukumar tara haraji ta yi kasa FIRS ta sanar da cewa, ta karbo kudin shiga Naira tiriliyan 10 a 2022, inda kudin da aka kashe a cikin kasafin kudi na 2023 suka kai Naira tiriliyan 21.83,inda aka samu gibin da ya kai na Naira tiriliyan 11.34.

Maganar dorewar bashin da kuma dai-daita tattalin arzikin Nijeriya a yanzu, ya rikewa Nijeriya Wuya ba kuma tare da yin wani fata mai kyau ba.

A bisa maganar gaskiya, kalubalen da tattalin arzikin Nijeriya ya ke a ciki a yanzu, zai koma ne kachkam, a kan WuyanTinubu bayan an rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayun 2003.
Sai dai, kwararru a fannin tattalin arziki sun yi nuni da cewa, akwai jan aiki wajen dai daita bashin da ake bin Nijeriya.

Daya daga cikin kwarraun Farfesa Bongo Adi ya shefawa kafara Daily Post cewa, bashin da gwamnatin Buhari ta ciwo wa kasar nan ya jinginar da makomar kasar ta hanyar nauyin da suka hau kanta.
Adi wanda Farfsan koyar da darasin tsimi da tanadi ne a Business School da ke a jihar Legos ya bayyana hakan ne a ranar Litinin da ta wuce, inda ya ci gaba da cewa, a kwanuka masu zuwa, tattalin arzikin Nijeriya zai yi wuya ya saith, domin gwamnatin Buhari ta tafi, ta bar kasar babu kudi.

Ya yi nuni da cewa, mafia daya ce, kawai gwamnatin mai zuwa ta tattauna kan ciwo bashi wanda dama ko a fadin duniya, an amince da yin irin wannan, musamman don gwamnatin ta rike darajarta.
A cewarsa,“Akwai kuma wani karin bashin dala miliyan 800 da gwamnatin ta karbo daga gun bankin duniya, ba tare da sanin ta ya ya ne, za ta biya shi ba ”

Ya kara da cewa, sun yi amfani da damar ciwo bashin ne kawai don raba shi a tsakanin su ganin cewa, suna shirin barin gwamnatin domin sun san, babu wanda zai ce sai sun biya shi.
Ya ce, babu sauran wani abu da za a yi magana kan cewa, Nijeriya ta riga ta ciyace, domin kwanukan da ke tafe, ba za su yi wani dadi ba akai.

Ya ce, manyan Likitocin da sauran kwararru a sauran fannoni suna ta ficewa daga kasar nan, shin wanene zai kirkiro da hanyoyin da za a biya bashin? abubuwan da ake sa ran za su taimaka wajen farfado da tattalin arzikin Nijeriya, duk sun durkushe.

A cewarsa,“Suna ci gaba tara mana bashi wanda hakan zai jefa rayuwar mu a cikin matsala, inda hakan ke nuna kamarin zai fi na gobe muni.”
Ya ci gaba da cewa, za su mika mataccen tattalin arziki ga gwamnatin Tinubu ne kawai ban san irin sihirin da Tinubu zai yi don tafiyar da kasar ba.

Ya sanar da cewa, Bankin duniya bai taba baiwa Nijeriya ko wasu kaashe masu taso wa kan aikin da za su yi ba.
Ya bayyana cewa, babban abinda keda mahimmanci shine, a bai wa ‘yan Nijeriya kwarin guiwa don su ci gaba da zama a cikin kasar, amma kafin hakan ta kasance, dole ne sai an saita tattalin arzikin kasar da tabbatar da tsaro tukunna.

Ya ce, kowacce kasa na zuba jari ne akan matasanta, amma abin takaici, lamarin ba haka yake a Nijeriya ba. Shin ata yaya ne, tattalin arzikin kasar zai tunbatsa ?
Shi ma wani kwararre a fannin tattalin arziki Dakta Ayo Teriba ya sanar da cewa, kuskuren da gwamnatin Buhari ta yi shine, yawan ciwo bashi, inda ya yi nuni da cewa, dole gwamnatin mai zuwa ya koyi darasi don gujewa sake mai-maita irin ‘yar gidan jiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalibai 947,000 Ne Za Su Rubuta Jarabawar JAMB Cikin Kwanaki 2

Next Post

Buhari Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Atiku Da Obi Suka Fadi Zaben 2023

Related

Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

1 hour ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

2 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

3 hours ago
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
Labarai

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

5 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

15 hours ago
Next Post
Buhari Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Atiku Da Obi Suka Fadi Zaben 2023

Buhari Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Atiku Da Obi Suka Fadi Zaben 2023

LABARAI MASU NASABA

Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.