Gwamnatin Jihar Gombe ta kaddamar da kwamiti mai mambobi 7 don rabawa da sayar da takin zamani na daminar bana ga manoman jihar domin saukaka wa manoma wajen samun Takin cikin sauki.
Lokacin da yake kaddamar da kwamitin ranar Alhamis a madadin Gwamnan Jihar, Muhammadu Inuwa Yahaya, Sakataren Gwamnatin Jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, ya bukaci kwamitin ya tabbatar da rabawa da sayar da takin akan lokaci ga manoma jihar.
- Ministar Jin Kai Ta Raba Wa Mata 3,500 Tallafin Kudi A Gombe
- Gwamnatin Gombe Za Ta Tallafa Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Funakaye
Sakataren ya ce ‘yan kwanaki bayan kaddamar da sayar da takin da gwamnan jihar ya yi a hukumance, gwamnatin jihar ta samo taki tirela 120, kimanin buhu dubu 72 kenan don rabawa manoman jihar.
“Aikin da aka daura muku ba wani mai wuya ba ne; karbar takin gwamnatin jihar tirela 120, da sanya ido wajen rarrabawa da sayar da shi a dukkan matakai, da kuma bai wa gwamnati shawarwarin da suka dace kan aikin da aka daura muku”. Cewar Sakataren gwamnatin Jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp