ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministar Jin Kai Ta Raba Wa Mata 3,500 Tallafin Kudi A Gombe

by Najib Sani a Gombe
4 years ago
Tallafi

Ministar jin kai da walwalar al’umma, Sadiya Farouk, a ranar Talata ta kaddamar da rabon tallafin kudi ga mata sama da 3,500 a jihar Gombe.

Ministar ta bada tallafin ne karkashin shirin taimakon mutane da suke fama da matsanancin talauci da ake wa lakabi ‘Conditional Cash Transfer’ (CCT) a turance.

  • NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan ‘Yan Bindiga 
  • An Harbe Dogarin Mataimakin Sufeton ‘Yansanda Yayin Wani Harin ‘Yan Bindiga A Kaduna

Da take jawabi a yayin kaddamar da rabon kudin tallafin a babban zauren taro na gidan gwamnatin Gombe, ministar ta bayyana cewa wadanda aka zaba don cin gajiyar tallafin za su karbi Naira 20,000 kowannensu.

ADVERTISEMENT

A cewarta, shirin tallafin na CCT na daya daga cikin abubuwan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kirkiro karkashin tsarin rage talauci da inganta walwalar al’ummar kasa, wanda yake mika taimako ga mutanen da suka fi fama da talauci musamman a yankunan karkara.

Ta yi ikirarin cewa gwamnatin Buhari ta gaji talauci wajen kaso saba’in daga gwamnatocin baya, shi yasa ta mayar da hankali wajen samar da hanyoyin rage wahalhalun jama’a.

LABARAI MASU NASABA

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

“Wannan shirin yana daga wadanda suka fi ko wanne tasiri a nahiyar Afrika wajen rage fatara a tsakanin al’umma da kuma janyo hadaka daga kasashen duniya don inganta rayuwar al’umma”. Inji ministar.

Sadiya ta kara da cewa ita da kanta ta ga mutanen da a baya suke cikin mawuyacin hali amma yanzu sun canza sakamakon wannan tallafin da aka basu a sassa daban-daban na kasar nan.

Shi ma da yake jawabi, gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahaya wanda mataimakin gwamnan, Manasseh Jatau, ya wakilce shi ya yaba wa gwamnatin tarayya bisa tallafin yana mai cewa tallafin zai kara wa wadanda suka ci gajiyarsa hanyoyin samun kudin shiga.

Ya kuma shawarci wadanda suka karbi tallafin da su yi amfani da kudin a kasuwanci da sana’oi da za su janyo musu riba.

Tallafi
Najib Sani a Gombe
+ postsBio
  • Najib Sani a Gombe
    https://hausa.leadership.ng/author/najib-sani-a-gombe/
    ‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Daba Masu Tu’annati Da Dare A Gombe

MASU ALAKA

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi
Addini

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

May 2, 2026
Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya
Kananan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Damu Kan Tsarin Yaki Da COVID-19 Bayan Sake Bullar Cutar A Nijeriya

April 28, 2026
Wakili Ya Rasu Kwana 3 Da Karewar Wa’adinsa A Matsayin Dan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi
Kananan Labarai

2027: Majalisar Dattawa Za Ta Ɗage Zaman Ta A Ranar Alhamis Saboda Zaɓen Fidda Gwani

April 28, 2026
Next Post
Ana Zaton Wuta A Makera…

Ana Zaton Wuta A Makera...

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.