• English
  • Business News
Sunday, June 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Kwara Ta Gargadi Manoman Kan Sayar Da Kayan Aikin Da Ta Ba Su

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

Gwamnatin Jihar Kwara, ta kaddamar da rabon kayan aikin gona ga manoma ‘yan asalin jihar su kimanin 2,019, inda ta gargade su a kan sayar da kayan da ta raba musu, domin amfanin kawunansu.

An gudanar da rabon wadannan kayan gona ne a garin Ilorin, wanda kuma yana daya daga cikin zango na uku na daukin aikin Fadama ‘CARES’ na gwamnatin jihar.

  • CISLAC Ta Gudanar Da Taro A Kano Kan Canjin Yanayi A Nijeriya
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Ceto Mutane 12 Da Dukiyar Miliyan 130 A Kano

Wasu daga cikin kayan da aka raba wa manoman sun hada da, injinan ban ruwa da abincin kajin gidan gona da sauran makamantansu.

A yayin kaddamar da rabon kayan, Gwamnan Jihar AbdulRahman AbdulRazak ya bayyana cewa, gwamnatinsa ta sama wa manoma wannan dauki ne, domin rage musu radadin tattalin arzikin da suke fuskanta tare kuma da yakar yunwa da talauci a daukacin fadin jihar baki-daya.
AbdulRahman ya ci gaba da bayyana cewa, gwamnatin jihar za ta tabbatar da ci gba da bibiyar kayan, domin manoman da suka amfana su su yi amfani da su yadda ya dace ba tare da sun sayarwa mutane daban ba.
Gwamnan, wanda shugaban kwamitin shiri na Fadama a jihar, Mista Ishiak Olayinka Oloruko-Oba ya wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa, ana sa ran aikin da manoman da suka amfana shi, zai taimakawa daukacin al’ummar jihar baki-daya.
A nasa jawabin tun da farko, jami’in shirin na ‘Fadama CARES’ na Jihar Kwara Fadama, Dakta Busari Toyin Isiaka ya bayyana cewa, shirin na daya daga cikin daukin annobar Korona da kuma kokarin sake farfado da tattalin arziki.
A cewar AbdulRahman, “A yau muna raba wa manoma su kimanin 2,019 wannan tallafi, inda ya kara da cewa, a shekarar 2022, manoma guda 6,561 ne suka amfana da shi, inda kuma manoma guda 8,020, suka fito a kashi na biyu.”
Daya daga cikin wadnda suka amfana da wadannan kayayyaki, akwai Kwamarade Jamiu Ahmed inda ya bayyana cewa, dukkanin daukacin wadannan kaya sun zo ne a kan gaba, inda kuma ya yi alkawarin yin amfani da kayan yadda ya dace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Akwai Tashoshin 5G Fiye Da Miliyan 3.5 A Kasar Sin

Next Post

Kasar Sin Ta Bukaci Isra’ila Da Ta Aiwatar Da Kudurin MDD Na Tsagaita Bude Wuta A Gaza

Related

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

5 hours ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

1 day ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

1 week ago
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Noma Da Kiwo

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

2 weeks ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

2 weeks ago
Next Post
Kasar Sin Ta Bukaci Isra’ila Da Ta Aiwatar Da Kudurin MDD Na Tsagaita Bude Wuta A Gaza

Kasar Sin Ta Bukaci Isra’ila Da Ta Aiwatar Da Kudurin MDD Na Tsagaita Bude Wuta A Gaza

LABARAI MASU NASABA

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

June 21, 2025
CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

June 21, 2025
Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

June 21, 2025
EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

June 21, 2025
Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna

Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna

June 21, 2025
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

June 21, 2025
Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika

Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika

June 21, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran

Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran

June 21, 2025
Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa

Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa

June 21, 2025
Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

June 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.