• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Yobe Ta Kashe N2.9bn Wajen Sayen Takin Zamani —kwamishina

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Jihar Yobe Ta Kashe N2.9bn Wajen Sayen Takin Zamani —kwamishina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Yobe, a ranar Asabar ta bayyana cewa ta kashe sama da Naira biliyan biyu da digo tara (N2.9bn) wajen siyo takin zamani tare da raba shi ga manoman jihar; tsakanin shekarar 2019 zuwa 2022.

Kwamishiniya a Ma’aikatar Noma da Albarkatun Kasa a jihar Yobe, Dakta Mairo Amshi, ita ce ta bayyana hakan a wani taron manema labarai a Damaturu.

  • Mutum 10 Sun Bace A Ruwa Sakamakon Kifewar Wani Kwale-Kwale A Yobe
  • Yadda Rugujewar Gadar Katarko Ta Katse Yobe Da Jihohin Borno Da Gombe

Dakta Mairo, ta ce gwamnatin jihar ta kashe Naira biliyan daya da digo biyar (N1.5bn) daga cikin jimlar kudin wajen siyan ton 3,000 na takin zamani samfurin NPK 20:10:10 a 2021.

Amshi ta kara da cewa yanzu haka ana ci gaba da rabon takin da kuma sayar da shi akan farashin naira 13,000 kan kowane buhu.

Bugu da kari kuma, ta ce gwamnatin jihar Yobe ta kashe Naira biliyan daya da digo hudu (N1.4bn) wajen siyo karin wasu ton 7,500 na NPK 15:15:15 a 2020. Wanda ta ce za a sayar wa manoman takin a kan Naira 5,000, kowace buhu, wanda kuma gwamnatin ta zabtare kashi 40 cikin 100 na farashin domin tallafa wa manoma.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

Ta bayyana cewa a 2019, gwamnati ta kashe Naira miliyan 882 wajen siyo motocin noma 40, tare da rabasu bashi kan naira miliyan 11 ga manyan manoma a jihar; wanda za a biya cikin shekaru hudu.

A hannu guda kuma, Dr Mairo Amshi ta ce gwamnatin jihar Yobe tare da hadin gwiwar kungiyar Red Cross (ICRC) sun yi wa shanu, tumaki, awaki da karnuka sama da miliyan 1.2 allurar rigakafin cutuka daban-daban a fadin jihar.

Da ta juya a fannin bunkasa kiwo a jihar, Kwamishiniyar ta ce gwamnatin jihar Yobe ta ce sun samu goyon bayan likitocin dabbobi 135, kwararru a kiyon lafiyar dabbobi 47, a wuraren kiwon dabbobi biyar da kuma ofisoshin kula da lafiyar dabbobi 17 a fadin jihar.

Har wala yau, Dr Amshi ta ce jihar tare da hadin gwiwar Ma’aikatar Noma da Raya Karkara ta Tarayya (FMARD) sun kafa cibiyoyin bunkasa wuraren kiwon dabbobi a Badegana da Gurjaje.

Amshi ta ce tuni an samar da kayayyakin aikin gudanar da cibiyoyin wadanda sun hada da rijiyoyin burtsatse, madatsun ruwa, asibitin dabbobi, wurin ciyar da abinci, tafkunan kiwon kifi, hanyoyin shiga, wutar lantarki, ingantattun magunguna da wuraren tattara madara da sauransu.

Hakazalika, Kwamishiniyar ta ce gwamnatin jihar Yobe ta gina cibiyar gudanar da bincike da kiwon dabbobi (LIBC) a Nguru domin bunkasa kiwon dabbobin.

A fannin noman rani kuma, ta ce gwamnatin jihar ba ta yi kasa a gwiwa ba wajen ganin an samu isasshen abinci, inda yanzu haka an samar da kadada (hectares) 2,000 na filayen noma a karkashin Shirin Noman LAVA a 2022 a jihar.

Haka kuma ta ce jihar Yobe tare da hadin gwiwar jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, sun kafa Cibiyar Binciken da Samar da Dabbobi ta Kasa (NAPRI) a Arewa Maso Gabas; a birnin Damaturu.

Kwamishinan ya kara da cewa jihar ta samu amincewar shiga shirin Gwamnatin Tarayya na Tallafin Dabbobin Dabbobi (Shirin L-Pres).


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zamu Rufe Filayen Jiragen Sama Har Sai An Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU – NANS

Next Post

Gwamnatin Kano Za Ta Kafa Hukumar Kula Da Magungunan Gargajiya

Related

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 
Manyan Labarai

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

2 hours ago
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

4 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

6 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Manyan Labarai

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

7 hours ago
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro
Manyan Labarai

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

8 hours ago
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar
Manyan Labarai

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

9 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Kafa Hukumar Kula Da Magungunan Gargajiya

Gwamnatin Kano Za Ta Kafa Hukumar Kula Da Magungunan Gargajiya

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.