ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Yobe Ta Kashe N2.9bn Wajen Sayen Takin Zamani —kwamishina

by Muhammad Maitela
4 years ago
Gwamnatin

Gwamnatin jihar Yobe, a ranar Asabar ta bayyana cewa ta kashe sama da Naira biliyan biyu da digo tara (N2.9bn) wajen siyo takin zamani tare da raba shi ga manoman jihar; tsakanin shekarar 2019 zuwa 2022.

Kwamishiniya a Ma’aikatar Noma da Albarkatun Kasa a jihar Yobe, Dakta Mairo Amshi, ita ce ta bayyana hakan a wani taron manema labarai a Damaturu.

  • Mutum 10 Sun Bace A Ruwa Sakamakon Kifewar Wani Kwale-Kwale A Yobe
  • Yadda Rugujewar Gadar Katarko Ta Katse Yobe Da Jihohin Borno Da Gombe

Dakta Mairo, ta ce gwamnatin jihar ta kashe Naira biliyan daya da digo biyar (N1.5bn) daga cikin jimlar kudin wajen siyan ton 3,000 na takin zamani samfurin NPK 20:10:10 a 2021.

ADVERTISEMENT

Amshi ta kara da cewa yanzu haka ana ci gaba da rabon takin da kuma sayar da shi akan farashin naira 13,000 kan kowane buhu.

Bugu da kari kuma, ta ce gwamnatin jihar Yobe ta kashe Naira biliyan daya da digo hudu (N1.4bn) wajen siyo karin wasu ton 7,500 na NPK 15:15:15 a 2020. Wanda ta ce za a sayar wa manoman takin a kan Naira 5,000, kowace buhu, wanda kuma gwamnatin ta zabtare kashi 40 cikin 100 na farashin domin tallafa wa manoma.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ta bayyana cewa a 2019, gwamnati ta kashe Naira miliyan 882 wajen siyo motocin noma 40, tare da rabasu bashi kan naira miliyan 11 ga manyan manoma a jihar; wanda za a biya cikin shekaru hudu.

A hannu guda kuma, Dr Mairo Amshi ta ce gwamnatin jihar Yobe tare da hadin gwiwar kungiyar Red Cross (ICRC) sun yi wa shanu, tumaki, awaki da karnuka sama da miliyan 1.2 allurar rigakafin cutuka daban-daban a fadin jihar.

Da ta juya a fannin bunkasa kiwo a jihar, Kwamishiniyar ta ce gwamnatin jihar Yobe ta ce sun samu goyon bayan likitocin dabbobi 135, kwararru a kiyon lafiyar dabbobi 47, a wuraren kiwon dabbobi biyar da kuma ofisoshin kula da lafiyar dabbobi 17 a fadin jihar.

Har wala yau, Dr Amshi ta ce jihar tare da hadin gwiwar Ma’aikatar Noma da Raya Karkara ta Tarayya (FMARD) sun kafa cibiyoyin bunkasa wuraren kiwon dabbobi a Badegana da Gurjaje.

Amshi ta ce tuni an samar da kayayyakin aikin gudanar da cibiyoyin wadanda sun hada da rijiyoyin burtsatse, madatsun ruwa, asibitin dabbobi, wurin ciyar da abinci, tafkunan kiwon kifi, hanyoyin shiga, wutar lantarki, ingantattun magunguna da wuraren tattara madara da sauransu.

Hakazalika, Kwamishiniyar ta ce gwamnatin jihar Yobe ta gina cibiyar gudanar da bincike da kiwon dabbobi (LIBC) a Nguru domin bunkasa kiwon dabbobin.

A fannin noman rani kuma, ta ce gwamnatin jihar ba ta yi kasa a gwiwa ba wajen ganin an samu isasshen abinci, inda yanzu haka an samar da kadada (hectares) 2,000 na filayen noma a karkashin Shirin Noman LAVA a 2022 a jihar.

Haka kuma ta ce jihar Yobe tare da hadin gwiwar jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, sun kafa Cibiyar Binciken da Samar da Dabbobi ta Kasa (NAPRI) a Arewa Maso Gabas; a birnin Damaturu.

Kwamishinan ya kara da cewa jihar ta samu amincewar shiga shirin Gwamnatin Tarayya na Tallafin Dabbobin Dabbobi (Shirin L-Pres).

Gwamnatin
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Kafa Hukumar Kula Da Magungunan Gargajiya

Gwamnatin Kano Za Ta Kafa Hukumar Kula Da Magungunan Gargajiya

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.