ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Yobe Ta Kashe N2.9bn Wajen Sayen Takin Zamani —kwamishina

by Muhammad Maitela
4 years ago
Gwamnatin

Gwamnatin jihar Yobe, a ranar Asabar ta bayyana cewa ta kashe sama da Naira biliyan biyu da digo tara (N2.9bn) wajen siyo takin zamani tare da raba shi ga manoman jihar; tsakanin shekarar 2019 zuwa 2022.

Kwamishiniya a Ma’aikatar Noma da Albarkatun Kasa a jihar Yobe, Dakta Mairo Amshi, ita ce ta bayyana hakan a wani taron manema labarai a Damaturu.

  • Mutum 10 Sun Bace A Ruwa Sakamakon Kifewar Wani Kwale-Kwale A Yobe
  • Yadda Rugujewar Gadar Katarko Ta Katse Yobe Da Jihohin Borno Da Gombe

Dakta Mairo, ta ce gwamnatin jihar ta kashe Naira biliyan daya da digo biyar (N1.5bn) daga cikin jimlar kudin wajen siyan ton 3,000 na takin zamani samfurin NPK 20:10:10 a 2021.

ADVERTISEMENT

Amshi ta kara da cewa yanzu haka ana ci gaba da rabon takin da kuma sayar da shi akan farashin naira 13,000 kan kowane buhu.

Bugu da kari kuma, ta ce gwamnatin jihar Yobe ta kashe Naira biliyan daya da digo hudu (N1.4bn) wajen siyo karin wasu ton 7,500 na NPK 15:15:15 a 2020. Wanda ta ce za a sayar wa manoman takin a kan Naira 5,000, kowace buhu, wanda kuma gwamnatin ta zabtare kashi 40 cikin 100 na farashin domin tallafa wa manoma.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ta bayyana cewa a 2019, gwamnati ta kashe Naira miliyan 882 wajen siyo motocin noma 40, tare da rabasu bashi kan naira miliyan 11 ga manyan manoma a jihar; wanda za a biya cikin shekaru hudu.

A hannu guda kuma, Dr Mairo Amshi ta ce gwamnatin jihar Yobe tare da hadin gwiwar kungiyar Red Cross (ICRC) sun yi wa shanu, tumaki, awaki da karnuka sama da miliyan 1.2 allurar rigakafin cutuka daban-daban a fadin jihar.

Da ta juya a fannin bunkasa kiwo a jihar, Kwamishiniyar ta ce gwamnatin jihar Yobe ta ce sun samu goyon bayan likitocin dabbobi 135, kwararru a kiyon lafiyar dabbobi 47, a wuraren kiwon dabbobi biyar da kuma ofisoshin kula da lafiyar dabbobi 17 a fadin jihar.

Har wala yau, Dr Amshi ta ce jihar tare da hadin gwiwar Ma’aikatar Noma da Raya Karkara ta Tarayya (FMARD) sun kafa cibiyoyin bunkasa wuraren kiwon dabbobi a Badegana da Gurjaje.

Amshi ta ce tuni an samar da kayayyakin aikin gudanar da cibiyoyin wadanda sun hada da rijiyoyin burtsatse, madatsun ruwa, asibitin dabbobi, wurin ciyar da abinci, tafkunan kiwon kifi, hanyoyin shiga, wutar lantarki, ingantattun magunguna da wuraren tattara madara da sauransu.

Hakazalika, Kwamishiniyar ta ce gwamnatin jihar Yobe ta gina cibiyar gudanar da bincike da kiwon dabbobi (LIBC) a Nguru domin bunkasa kiwon dabbobin.

A fannin noman rani kuma, ta ce gwamnatin jihar ba ta yi kasa a gwiwa ba wajen ganin an samu isasshen abinci, inda yanzu haka an samar da kadada (hectares) 2,000 na filayen noma a karkashin Shirin Noman LAVA a 2022 a jihar.

Haka kuma ta ce jihar Yobe tare da hadin gwiwar jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, sun kafa Cibiyar Binciken da Samar da Dabbobi ta Kasa (NAPRI) a Arewa Maso Gabas; a birnin Damaturu.

Kwamishinan ya kara da cewa jihar ta samu amincewar shiga shirin Gwamnatin Tarayya na Tallafin Dabbobin Dabbobi (Shirin L-Pres).

Gwamnatin
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Kafa Hukumar Kula Da Magungunan Gargajiya

Gwamnatin Kano Za Ta Kafa Hukumar Kula Da Magungunan Gargajiya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.