Rundunar sojojin Nijeriya ta yi nasarar kashe dan ta’addar nan mai suna, Boderi Isyaku, a tsakanin yankin Bada/Riyawa a kananan hukumomin Chikun da Igabi na jihar Kaduna.
Wata sanarwa da Kwamishinan ma’aikatar tsaro da harkokin cikin gida, Samuel Aruwan, ya sanya wa hannu a ranar Alhamis, ta ce gwamnatin jihar Kaduna ta tabbatar da chafke kasurgumin mai laifin bayan da jami’an tsaro suka gudanar da wani samame.
- ‘Ƴan bindiga Sun Kashe Mutum 12 A Kaduna
- Samar Da Jami’ar Musulunci A Jihar Kaduna Alheri Ne – Bola Ige
“Boderi, kamar yadda kowa ya san shi da sunan, ya shafe kusan shekaru goma yana yo wa al’amuran tsaro barazana ta hanyoyi da dama a jihar Kaduna da Jihar Neja.
Ya shahara wajen kai munanan hare-hare da sace-sacen jama’a da kashe-kashen da ba a saba gani ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp