• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa Sojojin Da Suka Kashe ‘Yan Bindiga 152 Tare Da Lalata Sansani 100

by Sadiq
3 years ago
Sojoji

Sojojin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’adda 152 tare da lalata sansaninsu sama da 100 a karo na biyu da na uku a 2022.

Mista Samuel Aruwan, Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kaduna, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a, yayin da yake gabatar da rahoton yanayin tsaro na kashi na biyu da na uku na shekarar 2022, ga gwamnan jihar, Malam Nasir El-Rufai.

  • ‘Gaskiyar Lamari Game Da Zargin Amfani Da Sinadarin Mercury A Rigakafin Yara’
  • Xi Ya Yi Jawabi Ga Taron COP14 Kan Kiyaye Filaye Masu Dausayi

Aruwan ya ce dakarun kasa da ke kewayen jihar sun kashe ‘yan bindiga 152.

A cewarsa, an kashe ‘yan bindiga da dama a lokacin da aka kai farmaki ta sama kan sansanonin da aka gano, inda ya ce an kashe ‘yan bindiga 16 a wani rikici a kananan hukumomin Birnin Gwari da Chikun, sannan an lalata sansanoni sama da 100 da ‘yan ta’adda suka mamaye.

Sai dai Aruwan ya ci gaba da cewa a cikin wannan lokaci jami’an tsaro sun ceto mutane 74 da aka yi garkuwa da su.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Ya kuma bayyana cewa, makaman da aka kama daga hannun ‘yan bindigar a cikin watanni shidan sun hada da, manyan bindigogi kirar GPMG guda biyu, AK-47 guda saba’in da hudu, AK-49 guda daya da kuma bindigogi kirar 06 guda tara.

Sauran sun hada da bindigogi masu wuta guda hudu, bindigogin fanfo guda hudu, bindiga g3 daya, bindigu na gida guda goma sha shida da kuma harsashi guda 5,398.

Ya kuma bayyana cewa an kwato haramtattun abubuwa daga hannun wadanda ake zargin.

Ya ce adadin haramtattun abubuwan da aka kama sun kai kilogiram 2,759.891 na tabar wiwi da miyagun kwayoyi.

Ya kara da cewa an samu ci gaba sosai a hanyar Kaduna zuwa Abuja, inda ya ce kashe-kashe da garkuwa da mutane a hanyar Kaduna zuwa Abuja ya ragu matuka a kashi na uku, ya kara da cewa kokarin hadin gwiwar yana samun sakamako mai kyau.

Aruwan, wanda ya bayyana godiyarsa ga kwamandoji, hafsoshi da jami’an tsaro da suke aiki dare da rana don ganin an kyautata wa kowa, ya kuma bukaci jami’an tsaro da kada su yi kasa a gwiwa, wajen dakile hare-hare.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi
Manyan Labarai

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Gargadi Masu Sayen Fili A Jikin BUK

Gwamnatin Kano Ta Gargadi Masu Sayen Fili A Jikin BUK

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.