Gwamnan jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf ya bayyana kudurin sake gina katafaren shatale-talen gidan gwamnatin jihar da aka rusa a kwanakin baya a wani wuri mafi da cewa – gadar Naibawa da ke wajen birnin jihar.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana hakan ne a yayin da yake gana wa da mai zanen shatale-talen ‘Golden Jubilee’ Kaltume Gana a sabon wurin da za a sake gina shatale-talen.
Gwamnan Yusuf ya sake nanata kudirin gwamnatisa na samar da ababen more rayuwa ga al’ummar jihar.
Ya ce wurin ya dace da zanen kuma ba zai haifar da wani kalubalen tsaro ba bayan gudanar da cikakken bincike, ya kuma sake tabbatar wa ‘yan jihar cigaba da samar da ayyukan more rayuwa masu inganci.
Mai zanen, Kaltume Gana ta gode wa gwamnan bisa yaba wa da aikinta na kwarewa da fasaha ta musamman.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp