• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

by Abubakar Sulaiman
1 month ago
Gwamnati

Gwamnatin Jihar Kogi ta zurfafa haɗin gwuiwa da hukumomin tarayya da kuma masu zuba jari na ƙasashen waje domin mayar da noma ginshiƙin a tattalin arziƙin jihar, da tabbatar da samar da wadataccen abinci da kuma fitar da amfanin gona zuwa ƙasashen waje.

Kwamishinan Noma da tsaro na abinci, Timothy Ojomah, ya bayyana haka a yayin ziyarar duba wata gona a Geregu, ƙaramar hukumar Ajaokuta, tare da ƙwararru da masu zuba jari, inda suka tattauna kan damar noman zamani da faɗaɗa kasuwa. Ya ce wannan tsari yana daidai da hangen nesa na Gwamna Usman Ododo wajen ƙarfafa manoma, samar da aiyukan yi, da kuma gina tattalin arziƙi mai ɗorewa.

  • NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo
  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki A Kogi, Ta Tsaida Aiyuka A Legas

A nasa jawabin, Mai ba wa Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin noma, Mathew Ajayi, ya ce haɗin gwuiwar ta yi daidai da shirin Shugaba Bola Tinubu na tabbatar da tsaron abinci da rage dogaro da shigo da kayan abinci daga ƙasashen waje. Ya ce an fi karkata hankali kan shinkafa, da masara, da waken soya da wasu amfanin gona da za a iya fitarwa zuwa ƙasashen waje.

Shugaban Hukumar Musayar Amfanin Gona ta Jihar Kogi, Victor Omofaiye, ya bayyana cewa hukumar za ta tabbatar da farashi mai adalci da samun damar kasuwannin waje ga manoma. A gefe guda kuma, Daraktan Onida Agri, Israel Kidron, ya ce Kogi ta dace da noman zamani saboda ƙasar ta mai albarka ce da kuma wadataccen ruwa. Ya ƙara da cewa kamfanin zai taimaka wajen horas da manoma da kawo fasahohi na zamani domin inganta amfanin gona.

Wannan haɗin gwuiwa ana sa ran zai ratsa wasu ƙananan hukumomi a jihar, inda zai samar da ayyukan yi, da ƙarfafa manoma, tare da mayar da Kogi ɗaya daga cikin manyan jihohin da ke taka rawa wajen sauya fasalin noma a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Next Post
Trump Ya Haramta Wa Jami’an Nijeriya Masu Cin Hanci Da Rashawa Shiga Amurka

Trump Ya Haramta Wa Jami'an Nijeriya Masu Cin Hanci Da Rashawa Shiga Amurka

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.