• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Neja Za Ta Fito Da Tsarin Ci gaban Jihar Na Shekaru 30

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Neja

Gwamnatin Jihar Neja ta kimtsa domin fito da wani tsarin ci gaba na shekaru 30 masu zuwa da za a aiwatar daki-daki har a cimma gaci.

Bologi Ibrahim, babban Sakataren watsa labarai na gwamna Mohammed Umaru Bago, shi ne ya sanar da hakan ta cikin sanarwar da ya fitar a garin Minna, ya ce, gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da ya ganawa da babban daraktan Bankin AfDB a Nijeriya, Lamin Barrow, a ofishinsa da ke Abuja.

  • Yanzu-yanzu: Gwamnan Neja Ya Mika Takardun Mika Gwamnati Ga Zababben Gwamna, Bago
  • Barayin Mutane Sun Tura Mutumin Da Suka Sace Ya Sayo Musu Man Fetur A Neja

Ganawar wacce aka yi ta kan gina wata kyakkyawar alakar aiki tsakanin Bankin da Gwamnatin jihar domin kawo ci gaba a jihar ta hanyar gina makarantu, tsarin dakile zaizayar kasa, makamashi da sauran fannoni.

Gwamna Umaru Bago, ya ce, a karon farko Gwamnatin jihar za ta samar da filin noma mai girman hekta 100,000 domin gudanar da ayyukan noma, kana za a fito da tsare-tsaren kyautata harkar noma da makamashi.

Gwamnan ya bayyana cewa, jihar Allah ya albarkaceta da dumbin albarkatun kasa, don haka gwamnatinsa za ta nemi masu zuba jari domin tabbatar da jihar ta amfana da dumbin albarkatun da Allah ya huwace musu.

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Gwamnan ya kuma tabbatar da cewa jihar za ta yi duk mai yiyuwa wajen saukaka wa masu zuba jari hanyoyin da za su samu zuwa jihar gudanar da kasuwancin domin haka ta cimma ruwa.

Lamin Barrow ya ce, tabbas hadakar za ta taimaka wajen kyautata rayuwar al’ummar jihar musamman a bangaren Ma’adinai.

Ya nuna kwarin guiwarsa na cewa Gwamnatin Bago tana da kwarewar da za ta iya cimma nasarorin kyautata rabon ribar demokradiyya ga al’umma ta yadda kowa zai mora.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Dalilin Da Ya Sa Kungiyar Sarrafa Taki Ta Bukaci Tinubu Ya Yi Bincike A Masana’antar

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar Sarrafa Taki Ta Bukaci Tinubu Ya Yi Bincike A Masana’antar

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.