ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Neja Za Ta Fito Da Tsarin Ci gaban Jihar Na Shekaru 30

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Neja

Gwamnatin Jihar Neja ta kimtsa domin fito da wani tsarin ci gaba na shekaru 30 masu zuwa da za a aiwatar daki-daki har a cimma gaci.

Bologi Ibrahim, babban Sakataren watsa labarai na gwamna Mohammed Umaru Bago, shi ne ya sanar da hakan ta cikin sanarwar da ya fitar a garin Minna, ya ce, gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da ya ganawa da babban daraktan Bankin AfDB a Nijeriya, Lamin Barrow, a ofishinsa da ke Abuja.

  • Yanzu-yanzu: Gwamnan Neja Ya Mika Takardun Mika Gwamnati Ga Zababben Gwamna, Bago
  • Barayin Mutane Sun Tura Mutumin Da Suka Sace Ya Sayo Musu Man Fetur A Neja

Ganawar wacce aka yi ta kan gina wata kyakkyawar alakar aiki tsakanin Bankin da Gwamnatin jihar domin kawo ci gaba a jihar ta hanyar gina makarantu, tsarin dakile zaizayar kasa, makamashi da sauran fannoni.

ADVERTISEMENT

Gwamna Umaru Bago, ya ce, a karon farko Gwamnatin jihar za ta samar da filin noma mai girman hekta 100,000 domin gudanar da ayyukan noma, kana za a fito da tsare-tsaren kyautata harkar noma da makamashi.

Gwamnan ya bayyana cewa, jihar Allah ya albarkaceta da dumbin albarkatun kasa, don haka gwamnatinsa za ta nemi masu zuba jari domin tabbatar da jihar ta amfana da dumbin albarkatun da Allah ya huwace musu.

LABARAI MASU NASABA

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Gwamnan ya kuma tabbatar da cewa jihar za ta yi duk mai yiyuwa wajen saukaka wa masu zuba jari hanyoyin da za su samu zuwa jihar gudanar da kasuwancin domin haka ta cimma ruwa.

Lamin Barrow ya ce, tabbas hadakar za ta taimaka wajen kyautata rayuwar al’ummar jihar musamman a bangaren Ma’adinai.

Ya nuna kwarin guiwarsa na cewa Gwamnatin Bago tana da kwarewar da za ta iya cimma nasarorin kyautata rabon ribar demokradiyya ga al’umma ta yadda kowa zai mora.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa
Labarai

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Next Post
Dalilin Da Ya Sa Kungiyar Sarrafa Taki Ta Bukaci Tinubu Ya Yi Bincike A Masana’antar

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar Sarrafa Taki Ta Bukaci Tinubu Ya Yi Bincike A Masana’antar

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.