• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ba Za Ta Lamunci Masu Zagon Kasa Su Durkusar Da Masana’antu Ba

by Bello Hamza
6 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ba Za Ta Lamunci Masu Zagon Kasa Su Durkusar Da Masana’antu Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwmnatin Tarayya ta yi kira ga masu ruwa da tsaki da shugabanni a fannin masana’antu, da su gudanar da shugabanci na gari tare da tabbatar da bin ka’ida, musamman domin a kara a habaka arzikin da ke a cikin nahiyar Afirka.

A cewar Gwamnatin, ba za ta kwale masu zagon kasa ko masu wata manufa su tarwatsa masana’antar ba.

  • Gwamnatin Tinubu Na Amfani Da Kuɗaɗen Tallafin Mai Don Ci Gaban Al’umma – Minista
  • Dalilan Da Suka Sa Gwamnan Kano Sallamar SSG Da Wasu Kwamishinoni 5

Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ne ya sanar da haka a jawabinsa a taron kaddamar da baje koli na kasa da kasa IEEER da aka gudanar a Abijan, Babban Birinin Kasar Coded’boire.

Kazalika, Shetrima ya bayyana cewa, wasu masu sanya ra’ayin kashin kansu a fannin gudanar da masana’antu ne ke janyo akuwar kalubale ga fannin da kuma janyo haddasa aukuwar rikice-rikice a yankunan da ke da albarkatun danyen mai

Shettima ya ci gaba da cewa, “Ba zan rungume hannu mu kyale irin wadannan masu yiwa fannin na masana’antu, zagon kasa ba, musamman don kar su samu damar cika burinsu”.

Labarai Masu Nasaba

FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

Mataikin ya kara da cewa, domin a takawa irin wadannan masu zagon kasar birki ne, Nijeriya ta samar da wani tsari na musamman domin a bai wa yankunan da ake hakar ma’adainai na kasar kariyar da ta kamata, musamman don a kara habaka fannin na ma’adanan kasar.

Ya sanar da cewa, Nijeriya Allah ya albarkace ta da Gwal da ya kai kashi 40 a cikin dari a fadin duniya.

Kazalika, Shettima ya sanar da cewa, Nijeriya na da yawan mai da ya kai kashi 10 a ciin dari, tare da kuma albarkatun kasa kamar irinsucobalt da lithium.

Sai dai, ya bayyana cewa, akwai irin wadannan albakatun kasar da har yanzu, ba a riga an tono su ba.

Mataimakin ya kuma bayar da tabbacin cewa, Nijeriya za ta ci gaba kula da masana’antun kasar, musamman domin a tabbatar da bin ka’ida da yin hadaka a kan kayan da ake sarrafawa a cikin kasar nan.

Taken taron shi ne, “Samar da Tsare-Tsare domin a kara habaka kayan da ake sarrafawa da kuma kula da masana’antar samar da makamashi”.

Shugabani da suka fito daga kasashen Afrika da dama ne suka halarci taron domin su tattauna kan yadda za su lalubo da mafita a fannin kirkier-kirkire da kuma kara kula da fannin samar da makamashi.

A cewar Mataimakin Shugaban kasar ba wai kawai ana magana ne a kan albarkatun kasa ba, batun ya kuma hada da yadda za a inganta rayuwar alumma da kuma samar masu da turba mai dorewa.

Ya sanar da cewa, idan aka samar da tsare-tsaren da suka kamata da bin ka’ida da kuma tabbatar da gaskiya, za a iya samun damar bunkasa fannin samar da mai mai makon kawo rabuwar kawuna.

Shettima ya ci gaba da cewa, Gwamnatin Tarayya a cikin sauye-sauyen da ta samar da ta kara habaka ayyukan Hukumar dake sa ido kan albarkatun ma’adanai ta kasa, wato NEITI.

Kazalika, Shettima ya bayar da tabbacin cewa, akwai bukatar kasashen da ke a nahiyar Afrika da ke fuskantar kalubale iri daya da su mayar da hankali wajen lalubo da hanyoyin magance kalubalen.

Mataimakin Shugaban kasar ya sanar da cewa, sake samar da sauye-sauyen da Gwamnatin Tarayya ta yi a kamfanin man fetur na kasa NNPCL a karkashin dokar da ke tafiyar da masana’antar sarrafa man fetur ta 2021, hakan ya sanya kamfanin ya mayar da hankali wajen hada-hadar kasuwanci man wanda hakan ya kara habaka fannin na man.

Ya sanar da cewa, a yanzu kamfnin na NNPC, na gudanar da ayyukansa ne kai tsaye, ba tare da shishigin bangaren Gwamnatin Tarayya ba.

Mataimakin Shugaban kasar ya kuma jaddada mahimmancin gudunmawa kayan da ake sarrafawa a kasar suke da shi, musamman wajen kara bunkasa tattalin arzikin kasar.

Shettima ya sanar da cewa, ta hanyar dokar kayan da ake sarrafawa a cikin kasar nan ta 2010, Nijeriya ta samu damar kara shiga fannin samar da man fetur da iskar Gas wanda ya kai daga kashi 5 a cikin dari, zuwa kashi 30 a cikin dari.

Ya sanar da cewa, bisa nasarar da aka samu ta kafa matatar mai ta Dangote wacce kuma ta kasance mafi girma, a hakan ya sanya Nijeriya za ta iya kara mayar da hankali wajen sarafa kayan cikin gida.

Shi ma a na sa jawabin a wajen taron Mataimakin Shugaban kasar Côte d’Iboire, Tremoko Meyliet Kone, ya bayyana jin dadinsa kan ziyarar aikin da Shettima da sauran baki da suka halarci taron.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Shettima
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN : Sin Ta Shirya Cimma Burin Samun Ci Gaba Na Shekara-Shekara, Masu Bayyana Ra’ayoyinsu Na Da Karfin Gwiwa Game Da Hasashen Tattalin Arzikin Sin

Next Post

Yadda Mutuwar Faraɗ-ɗaya Ke Farmakar ‘Yan Nijeriya

Related

FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista
Manyan Labarai

FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

37 minutes ago
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara
Labarai

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

9 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

12 hours ago
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

13 hours ago
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 
Manyan Labarai

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

14 hours ago
Labarai

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

17 hours ago
Next Post
Yadda Mutuwar Faraɗ-ɗaya Ke Farmakar ‘Yan Nijeriya

Yadda Mutuwar Faraɗ-ɗaya Ke Farmakar 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

June 3, 2025
An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

June 2, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

June 2, 2025
Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.