• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

by Abubakar Abba and Sulaiman
4 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya tare da hadin gwiwar Gidauniyar Bunkasa Aikin Gona ta Kasa da Kasa (IFAD)na kokarin samar da wata manhajar zamani ga manoman Nijeriya, domin fara tantance su.

Hadakar, za ta bayar da damar yi wa manoman kasar nan rijista, wacce za ta bayar da damar gano kowanne manomi da gonakinsa da irin kasar noman da yake amfani da ita da kuma irin nau’in amfanin gonar da yake nomawa.

  • Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
  • 2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Haka zalika, za a shigo da sashen samar da bayanai da kuma hukumar da ke rajistar katin dan kasa (NIMC), domin gudanar da wannan aiki.

Manhajar za kuma ta sama wa manoman kasar damar samun kudade a matsayin rance ba tare da wani bata lokaci ba daga wajen gwamnati.

Kazalika, ana sa ran aikin zai tattaro daukacin manoman da ke kasar da kuma samun bayanan kafatanin manoman da ke jihohi 36 na wannan kasa, ciki har da babban birnin tarayyar Abuja.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

A jawabinsa a wajen taron kaddamar da tsarin tattaunawa kan shirin yin amfani da fashar zamani na samar da yin rjitsar ta manoman kasar (NDFR), wadda aka gudanar a babban birnin tarayyar Abuja, Babban Sakatare a Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Dakta Marcus Ogunbiyi, ya bayyana cewa; sabon tsarin zai taimaka matuka, wajen rage duk wani matsayi da manoman kasar suke ciki, musamman manoman da ba su mallaki wata gona ba.

“Za mu tabbatar mun yi rijistar sunayen manoman kasar da kuma gonakinsu, sannan kuma ba wai kawai yin rijistar ba, har da irin nau’in amfanin da suke nomawa da kuma nau’in irin kasar da ke gonakin nasu,” in ji Marcus.

Dakta Marcus ya kara da cewa, babu wata gona da ba ta da manomi, amma akwai manoma da dama da ba su mallaki gonaki ba.

“Idan mun yi wa manoman rijistar, za mu raba musu Kati kai tsaye da kuma wani Katin na manhajar zamani, domin a rika yin aiki da manoman kai tsaye ta yadda za a iya saurin gano kowane manomi a cikin sauki,” a cewar Marcus.

Ya ci gaba da cewa, hakan zai bayar da damar samun adana bayanansu kai tsaye da ya kunshi na sheda, musamman domin su rika samun taimakon daga wurin gwamnat da ya hada da samun rancen kudin yin noma.

Markus ya bayyana cewa, domin samun cin nasarar wannan aiki, Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abincii, ta dauki wasu matakai domin samun bayanan manoman kasar tare da adana bayannan nasu.

Ya ci gaba da cewa, guda daga cikin dabarun aikin shi ne, na yin hadaka da hukumar da ke rajistar katin dan kasa (NIMC), musamman domin wanzar da wannan aiki na yi wa manoman rijista da kuma tattara bayanansu, domin tabbatar da ganin kowane manomi, an sanya shi a cikin tsarin.

Ita kuwa a nata jawabin, Daraktar IFAD a kasar nan, Madam Dede Ahoefa Ekoue ta bayyana cewa, sashen samar da abinci na Majalisar Dinkin Duniya, na alfaharin kasancewa cikin wannan sabon shirin.

“Gundunmawarmu ita ce, kokarin samun damar jawo sauran abokan hadaka na gwamnati da kuma masu kamfanoni masu zaman kansu, ta yadda za su zuba kudade tare, domin taimaka wa kokarin gwamnatin kasar, na yin rijistar manoman kasar,“ in ji Dede.

Madam Dede ta kara da cewa, koda-yake a baya, an yi irin wannan kokarin, amma ya kamata a ci gaba da wannan shirin, duba da muhimmancin da yake da shi.

“A yanzu, gwamnatin kasar ta samar mana da wata alkibla da kuma umartar daukacin masu ruwa da tsaki a fannin aikin noman kasar, domin a yi aiki tare,“ in ji ta.

Ta sanar da cewa, irin wannan aikin ne muke yi da sauran abokan hadaka kamar irin su; Bankin Raya Nahiyar Afrika, Hukumar Bunkasa Samar da Wadataccen Abinci, Bankin Duniya, Tarayyar Turai, Bankin Bunkasa Musulunci da kuma Gwamnatin Burtaniya.

Kazalika, ta sanar da cewa; babbin abin shi ne, ta hanyar yin aiki da kungiyoyin manoman kasar nan, domin su ne za su amfana da aikin.

Madam Dede ta ci gaba da cewa, hukumar ta IFAD, na matukar farin cikin jawo abokan hadaka da sauran sassan ma’aikatun gwamnati da sauran hukomomin gwamnatin kasar, domin tafiya tare cikin aikin.

Ta yi nuni da cewa, wannan aiki zai kasance tamkar samar da wani sauyi ne na ci gaba ga fanin aikin noman kasar.

Shi ma a nasa jawabin, Darakan kungiyar kasa da kasa ta Heifer da ke aiki a kasar nan, Dakta Lekan Tobe ya bayyana babban muhimancin da ke tattare da aikin, musamman ta hanyar yin hadaka.

Ya sanar da cewa, wannan aikin na daga cikin wasu shawarwarin da aka bayar a baya, wanda gwamnatin kasar nan ta yi hadaka da nufin yin amfani da fasahar zamani, domin a kara samar da wadataccen abinci a kasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Next Post

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

14 hours ago
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

15 hours ago
Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

1 day ago
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

1 week ago
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

3 weeks ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

3 weeks ago
Next Post
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A Kuɗin Naira

September 27, 2025
Shugaban Cuba Ya Yi Bayani Kan Nazarin Fasahohin Sin A Fannoni Shida

Shugaban Cuba Ya Yi Bayani Kan Nazarin Fasahohin Sin A Fannoni Shida

September 27, 2025
Bukatar Mutane Su Kula Da Warin Jikinsu

Bukatar Mutane Su Kula Da Warin Jikinsu

September 27, 2025
Me Ya Sa Kamfanonin Jamus Fiye Da 560 Suka Zabi Wani Gari A Kasar Sin Don Gudanar Da Harkokinsu?

Me Ya Sa Kamfanonin Jamus Fiye Da 560 Suka Zabi Wani Gari A Kasar Sin Don Gudanar Da Harkokinsu?

September 27, 2025
Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

September 27, 2025
Firaministan Sin: Adalci Shi Ne Abu Mafi Daraja A Wurin Kasashen Duniya 

Firaministan Sin: Adalci Shi Ne Abu Mafi Daraja A Wurin Kasashen Duniya 

September 27, 2025
Yadda Ake Hada Sushi

Yadda Ake Hada Sushi

September 27, 2025
Ribar Da Manyan Kamfanonin Kasar Sin Ke Samu Ta Dawo Turbar Karuwa A Watanni 8 Na Farkon Bana

Ribar Da Manyan Kamfanonin Kasar Sin Ke Samu Ta Dawo Turbar Karuwa A Watanni 8 Na Farkon Bana

September 27, 2025
Atletico Madrid Ta Zazzaga Wa Real Madrid Ƙwallaye 5 A Metropolitano

Atletico Madrid Ta Zazzaga Wa Real Madrid Ƙwallaye 5 A Metropolitano

September 27, 2025
Tawagar Gwamnatin Tsakiya Na Ci Gaba Da Ziyartar Jami’ai Da Mazauna Yankuna Da Dama Na Jihar Xinjiang

Tawagar Gwamnatin Tsakiya Na Ci Gaba Da Ziyartar Jami’ai Da Mazauna Yankuna Da Dama Na Jihar Xinjiang

September 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.