• English
  • Business News
Monday, September 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Na Shiri Da Ƴan Bindiga, Tana Ba Su Biliyoyi — El-Rufai

by Abubakar Sulaiman
2 hours ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Na Shiri Da Ƴan Bindiga, Tana Ba Su Biliyoyi — El-Rufai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna kuma tsohon Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Malam Nasir El-Rufai, ya zargi gwamnatin tarayya da zaɓar hanya biyan kuɗaɗe da samar da kayan tallafi ga ƴan bindiga ƙarƙashin abin da ake kira dabarar “non-kinetic” wajen yaƙi da rashin tsaro. Ya bayyana cewa wannan tsari ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro (ONSA) ne ke jagoranta, tare da jaddada cewa akwai hujjojin tabbatar da hakan.

A yayin tattaunawa a shirin Sunday Politics na gidan talabijin ɗin Channes, El-Rufai ya bayyana cewa gwamnati na bai wa ƴan bindiga kuɗi da kayan abinci, lamarin da ya kira “tallafa wa ta’addanci”. Ya ce ba zai taɓa amincewa da irin wannan dabarar ba. “Abin da ba zan taɓa yi ba shi ne in biya ƴan bindiga, in riƙa ba su tallafi na kudi da abinci da sunan hanyar magance ta’addan ba da ƙarfin Soji ba. Wannan wauta ce. Tamkar muna ƙarfafar su ne,” in ji shi.

  • Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai
  • Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

El-Rufai ya jaddada cewa wannan tsari ba ya fitowa daga gwamnatin Kaduna kai tsaye, sai dai daga Abuja. A cewarsa, “Ba gwamnatin Kaduna ba ce, manufar gwamnatin ƙasa ce da ONSA yasa gaba, kuma Kaduna na ciki. Jihohi da dama sun nuna rashin amincewa, amma wannan ce manufar yanzu — rungumar ƴan bindiga.”

Tsohon gwamnan, wanda ya daɗe yana fafutukar a yi amfani da ƙarfin Soji wajen murƙushe ƴan ta’adda, ya sake jaddada matsayinsa cewa “duk wani tubabben ɗan bindiga shi ne wanda aka kashe. Mu kashe su, mu buga da su, mu kawar da su baki ɗaya, sannan idan akwai kashi biyar cikin ɗari da suke son gyara, sai a taimaka musu. Ba za ka taba yin sulhu da maƙiya daga fuskar rauni ko tsoronsa ba, kuma ba za ka ba su kuɗi su je su sayi muggan makamai ba.”

Ya kuma yi gargaɗi cewa muddin wannan manufar biyan kuɗaɗen da neman sulhu da ƴan bindiga na ci gaba, matsalar rashin tsaro a Arewacin Nijeriya ba za ta gushe ba. El-Rufai ya kuma zargi gwamnatin Kaduna ta yanzu da gazawa wajen kare al’umma, yana mai cewa an riƙa biyan kuɗaɗen fansa masu yawan gaske a asirce. “Ni na yi gwamna shekaru takwas, makarantu uku kacal aka kai wa hari. Wannan gwamnati ta shafe shekaru biyu amma fiye da hakan aka kai wa hari. An biya biliyoyin Naira a matsayin kuɗin fansa. Idan gwamnati ko kowa zai musanta, muna da hujjoji, kuma zamu bayyana su lokacin da ya dace,”in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai

An Lalata Tamfatsetsiyar Gonar Wiwi A Taraba Tare Da Kama Dan Shekaru 70 A Anambra 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCEl-RufaiNuhu RibaduTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai

Next Post

Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai

Related

Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai
Manyan Labarai

Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai

56 minutes ago
An Lalata Tamfatsetsiyar Gonar Wiwi A Taraba Tare Da Kama Dan Shekaru 70 A Anambra 
Manyan Labarai

An Lalata Tamfatsetsiyar Gonar Wiwi A Taraba Tare Da Kama Dan Shekaru 70 A Anambra 

21 hours ago
Legas Ta Laƙume Aikin Naira Tiriliyan 3.9 Cikin Shekaru Biyun Tinubu
Manyan Labarai

Legas Ta Laƙume Aikin Naira Tiriliyan 3.9 Cikin Shekaru Biyun Tinubu

2 days ago
A Karo Na 3 Cikin Wata Guda, Jirgin Ruwa Ya Sake Kifewa A Sakkwato
Manyan Labarai

A Karo Na 3 Cikin Wata Guda, Jirgin Ruwa Ya Sake Kifewa A Sakkwato

2 days ago
Gwamnatin Katsina Za Ta Sayo Babura 700 da Motoci 20 Don Samar Da Tsaro
Manyan Labarai

Gwamnatin Katsina Za Ta Sayo Babura 700 da Motoci 20 Don Samar Da Tsaro

2 days ago
Mutane Da Dama Sun Ɓace Yayin Da Jirgin Ruwa Ya Kife A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutane Da Dama Sun Ɓace Yayin Da Jirgin Ruwa Ya Kife A Sakkwato

3 days ago
Next Post
Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai

Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara - El-Rufai

LABARAI MASU NASABA

Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai

Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai

September 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shiri Da Ƴan Bindiga, Tana Ba Su Biliyoyi — El-Rufai

Gwamnatin Tarayya Na Shiri Da Ƴan Bindiga, Tana Ba Su Biliyoyi — El-Rufai

September 1, 2025
Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai

Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai

September 1, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 

Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 

August 31, 2025
Xi Jinping Da Uwargidansa Peng Liyuan Sun Shirya Liyafar Maraba Da Baki Na Kasa Da Kasa Ga Mahalarta Taron SCO

Xi Jinping Da Uwargidansa Peng Liyuan Sun Shirya Liyafar Maraba Da Baki Na Kasa Da Kasa Ga Mahalarta Taron SCO

August 31, 2025
Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

August 31, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Farfado Da Kasa Bisa Karfin Ruhin Turjiya Ga Zalunci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Farfado Da Kasa Bisa Karfin Ruhin Turjiya Ga Zalunci

August 31, 2025
Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

August 31, 2025
Kasar Sin Ta Inganta Wuraren Tunawa Da Tarihi Don Bikin Samun Nasara Kan Zaluncin Japanawa

Kasar Sin Ta Inganta Wuraren Tunawa Da Tarihi Don Bikin Samun Nasara Kan Zaluncin Japanawa

August 31, 2025
Jami’an Senegal Sun Yaba Da Ci Gaban Da Aka Samu Wajen Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing

Jami’an Senegal Sun Yaba Da Ci Gaban Da Aka Samu Wajen Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing

August 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.