• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Na Shiri Da Ƴan Bindiga, Tana Ba Su Biliyoyi — El-Rufai

by Abubakar Sulaiman
2 months ago
Tarayya

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna kuma tsohon Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Malam Nasir El-Rufai, ya zargi gwamnatin tarayya da zaɓar hanya biyan kuɗaɗe da samar da kayan tallafi ga ƴan bindiga ƙarƙashin abin da ake kira dabarar “non-kinetic” wajen yaƙi da rashin tsaro. Ya bayyana cewa wannan tsari ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro (ONSA) ne ke jagoranta, tare da jaddada cewa akwai hujjojin tabbatar da hakan.

A yayin tattaunawa a shirin Sunday Politics na gidan talabijin ɗin Channes, El-Rufai ya bayyana cewa gwamnati na bai wa ƴan bindiga kuɗi da kayan abinci, lamarin da ya kira “tallafa wa ta’addanci”. Ya ce ba zai taɓa amincewa da irin wannan dabarar ba. “Abin da ba zan taɓa yi ba shi ne in biya ƴan bindiga, in riƙa ba su tallafi na kudi da abinci da sunan hanyar magance ta’addan ba da ƙarfin Soji ba. Wannan wauta ce. Tamkar muna ƙarfafar su ne,” in ji shi.

  • Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai
  • Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

El-Rufai ya jaddada cewa wannan tsari ba ya fitowa daga gwamnatin Kaduna kai tsaye, sai dai daga Abuja. A cewarsa, “Ba gwamnatin Kaduna ba ce, manufar gwamnatin ƙasa ce da ONSA yasa gaba, kuma Kaduna na ciki. Jihohi da dama sun nuna rashin amincewa, amma wannan ce manufar yanzu — rungumar ƴan bindiga.”

Tsohon gwamnan, wanda ya daɗe yana fafutukar a yi amfani da ƙarfin Soji wajen murƙushe ƴan ta’adda, ya sake jaddada matsayinsa cewa “duk wani tubabben ɗan bindiga shi ne wanda aka kashe. Mu kashe su, mu buga da su, mu kawar da su baki ɗaya, sannan idan akwai kashi biyar cikin ɗari da suke son gyara, sai a taimaka musu. Ba za ka taba yin sulhu da maƙiya daga fuskar rauni ko tsoronsa ba, kuma ba za ka ba su kuɗi su je su sayi muggan makamai ba.”

Ya kuma yi gargaɗi cewa muddin wannan manufar biyan kuɗaɗen da neman sulhu da ƴan bindiga na ci gaba, matsalar rashin tsaro a Arewacin Nijeriya ba za ta gushe ba. El-Rufai ya kuma zargi gwamnatin Kaduna ta yanzu da gazawa wajen kare al’umma, yana mai cewa an riƙa biyan kuɗaɗen fansa masu yawan gaske a asirce. “Ni na yi gwamna shekaru takwas, makarantu uku kacal aka kai wa hari. Wannan gwamnati ta shafe shekaru biyu amma fiye da hakan aka kai wa hari. An biya biliyoyin Naira a matsayin kuɗin fansa. Idan gwamnati ko kowa zai musanta, muna da hujjoji, kuma zamu bayyana su lokacin da ya dace,”in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi
Manyan Labarai

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
Next Post
Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai

Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara - El-Rufai

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.