• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

by Sadiq
4 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bukaci cibiyoyin da ke bayar da rancen kudaden noma, da su kirikiro da tsarin da zai taimaka wa kananan manoma masu renon tsirrai, domin samar da tsirran masu tarin yawa a fadin wannan kasa.

Ministan Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wdataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ne ya gabatar da wannan bukata a taron bita, domin samar da rance ga manoman da ke fannin renon tsirran.

  • ‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu
  • El-Rufai Ya Zargi Bangaren Shari’a Da Cin Hanci Da Rashawa

Kungiyar Masu Renonin Tsirrai ta Kasa (HortiNigeria) ce, ta shirya taron bisa hadaka da ‘HortiNigeria’ da hukumar bayar da bashin kayan noma, don habaka shi (NIRSAL) da aka gudanar a babban birnin tarayyar, Abuja.

“Muna da bukatar samar da rancen kudade ga manoman da ke wannan fanni, musamman kanana domin su zuba jarin na dogon zango a fannin”, in ji Kyari.

Sanata Kyari ya yi nuni da cewa, renon tsirrai da kuma noman kayan Lambu, wani bangare ne da ke taimaka wa fannin aikin noman kasar.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

“Fanin na kuma taimaka wa wajen samar da ayyukan yi da samar da abinci mai gina jikin Dan’adam da kuma bunkasa hada-hadar kasuwanci, musamman duba da wayar da kai da ake yi na samar da abinci mai gina jiki,“ in ji shi.

Shi ma, a nasa jawabin a wajen taron, Daraktan Cibiyar Bunkasa Samar da Takin Zamni ta Kasa da Kasa (IFDC) da ke kasar nan, Dakta Yusuf Dramani ya bayyana cewa; cibiyar na aiki kafada da kafada da Hukumar NIRSAL, musamman don cike gibin da ake da shi a kasar, wajen samar da rancen kudaden noma ga manoman kasar.

“Duk da cewa, fannin aikin noma na kasar nan, na bayar da gagarumar gudunmawa wajen kara bunkasa fannin tattalin arzikin kasar da kuma samar da ayyukan yi ga ‘yan kasar, amma abin takaici ne ganin yadda ake fuskantar kalubalen rashin samun rancen kudaden noma, musamman a fannin noman renon tsirrai.

“Mun yi amanna da cewa, za a iya sauya wadannan kalubalen da ake fuskanta na samar da rancen kudaden zuwa ga damarmaki, idan har cibiyoyin da ke bayar da rancen kudaden noman sun samar da kayan aikin da suka dace da ilimin da tsare-tsaren da suka kamata da sauransu,” in ji Yusuf.

Ya alakanta gudanar da taron da cewa, abu ne da ya zo kan gaba kuma mai muhimmancin gaske, wanda hakan zai bai wa cibiyoyin da suka halarci taron damar sanin yadda ake gudanar da hada-hadar kasuwanci a fannin na renon tsirrai da kuma irin dimbin damammakin da ke cikin fannin.

Shi kuwa, daraktan gudanar da shirye-shiye na kungiyar ta ‘HortiNigeria’ ta kasa, Mohammed Salasi Idris ya bayyana cewa, manufar da kungiyar ke son cimma, ita ce ta samar da damar samo rancen da ya kai kimanin Yuro miliyan 6, inda ya sanar da cewa, a yanzu mun kai sama da kashi 50 cikin 100 na wannan adadin kudi.

Da yake yin tsokaci kan kalubalen da ake fuskanta a fannin ya sanar da cewa, tsarin samar da rancen kudi na MPR da ke karkashin Babban Bankin Kasa (CBN), ya kara kudin ruwa na bayar da rancen kudin noma daga kashi 18 cikin 100 zuwa kashi 27 cikin 100, inda ya sanar da cewa; wannan babban kalubale ne ga wadanda suke fannin na renon tsirran.

Kazalika, ya sanar da cewa, wani karin kalubalen da manoman da ke Arewacin kasar nan ke fusanta shi ne, na tsadar biyan Leburori.

“Akasarin Leburorinmu, bisa rahotannin da muke samu shi ne, suna zuwa ne daga wasu iyakokin kasar nan, sannan kuma ga yadda darajar Naira ta fadi, inda ya kara da cewa; a cikin shekaru biyu zuwa uku, ba mu ji da dadi ba; musamman ganin yadda darajar Naira ta fadi warwas, kan takardar CFA, wanda hakan ya sa biyan aikin da Leburorin suka yi ya karu”, in ji Idris.

Shi kuwa, a nasa jawabin a wajen taron Jakadan Kasar Netherlands a Nijeriya, Bengt ban Loosdrecht, ya bayyana cewa; fannin na renon tsirrai na taimakawa wajen kara bunkasa tattalin arzikin kasar da samar da aikin yi tare kuma da samar da abinci mai gina jiki.

Sai dai, Jakadan ya yi nuni da cewa; za a iya samun hakan ne, kawai idan aka samar da rancen kudade ga wadanda suke cikin fannin, wanda ita ce kadai mafita.

Bengt ban Loosdrecht, wanda Mista Folusho Adejoro, Mai Bayar da shawara a bangaren samar da wadataccen abinci da rage dumamar yanayi a ofishin Jakadancin kasar ta Netherlands a Nijeriya ya wakilce shi a wajen taron, ya bayyana cewa, manoma da dama a wannan fannin, na yin aiki tukuru, sai dai, suna fuskantar kalubalen samun rancen kudin renon na tsirrai.

Ya ci gaba da cewa, manufar taron shi ne, domin cike gibin da ake da shi na samar da damar samun rancen kudaden, wanda hakan zai bai wa bankuna da sauran cibiyoyin bayar da rancen kudaden noma fahimtar damar da ke cikin wannan fanni.

Ofishin Jakadanci na kasar ta Netherlands da ke kasar nan ce ke bayar da dauki a shirin habaka renonin tsirrai, wanda aka faro shirin tun a 2021 zuwa 2025, musaman domin tallafa wa fannin tare da samar da wadataccen abinci mai gina jiki a daukacin fadin Nijeriya baki-daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kuɗi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

Next Post

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

Related

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

1 day ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

1 day ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

1 week ago
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

1 week ago
Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

1 week ago
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

2 weeks ago
Next Post
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.