ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

by Sadiq
1 year ago
Manoma

Gwamnatin tarayya ta bukaci cibiyoyin da ke bayar da rancen kudaden noma, da su kirikiro da tsarin da zai taimaka wa kananan manoma masu renon tsirrai, domin samar da tsirran masu tarin yawa a fadin wannan kasa.

Ministan Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wdataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ne ya gabatar da wannan bukata a taron bita, domin samar da rance ga manoman da ke fannin renon tsirran.

  • ‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu
  • El-Rufai Ya Zargi Bangaren Shari’a Da Cin Hanci Da Rashawa

Kungiyar Masu Renonin Tsirrai ta Kasa (HortiNigeria) ce, ta shirya taron bisa hadaka da ‘HortiNigeria’ da hukumar bayar da bashin kayan noma, don habaka shi (NIRSAL) da aka gudanar a babban birnin tarayyar, Abuja.

ADVERTISEMENT

“Muna da bukatar samar da rancen kudade ga manoman da ke wannan fanni, musamman kanana domin su zuba jarin na dogon zango a fannin”, in ji Kyari.

Sanata Kyari ya yi nuni da cewa, renon tsirrai da kuma noman kayan Lambu, wani bangare ne da ke taimaka wa fannin aikin noman kasar.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

“Fanin na kuma taimaka wa wajen samar da ayyukan yi da samar da abinci mai gina jikin Dan’adam da kuma bunkasa hada-hadar kasuwanci, musamman duba da wayar da kai da ake yi na samar da abinci mai gina jiki,“ in ji shi.

Shi ma, a nasa jawabin a wajen taron, Daraktan Cibiyar Bunkasa Samar da Takin Zamni ta Kasa da Kasa (IFDC) da ke kasar nan, Dakta Yusuf Dramani ya bayyana cewa; cibiyar na aiki kafada da kafada da Hukumar NIRSAL, musamman don cike gibin da ake da shi a kasar, wajen samar da rancen kudaden noma ga manoman kasar.

“Duk da cewa, fannin aikin noma na kasar nan, na bayar da gagarumar gudunmawa wajen kara bunkasa fannin tattalin arzikin kasar da kuma samar da ayyukan yi ga ‘yan kasar, amma abin takaici ne ganin yadda ake fuskantar kalubalen rashin samun rancen kudaden noma, musamman a fannin noman renon tsirrai.

“Mun yi amanna da cewa, za a iya sauya wadannan kalubalen da ake fuskanta na samar da rancen kudaden zuwa ga damarmaki, idan har cibiyoyin da ke bayar da rancen kudaden noman sun samar da kayan aikin da suka dace da ilimin da tsare-tsaren da suka kamata da sauransu,” in ji Yusuf.

Ya alakanta gudanar da taron da cewa, abu ne da ya zo kan gaba kuma mai muhimmancin gaske, wanda hakan zai bai wa cibiyoyin da suka halarci taron damar sanin yadda ake gudanar da hada-hadar kasuwanci a fannin na renon tsirrai da kuma irin dimbin damammakin da ke cikin fannin.

Shi kuwa, daraktan gudanar da shirye-shiye na kungiyar ta ‘HortiNigeria’ ta kasa, Mohammed Salasi Idris ya bayyana cewa, manufar da kungiyar ke son cimma, ita ce ta samar da damar samo rancen da ya kai kimanin Yuro miliyan 6, inda ya sanar da cewa, a yanzu mun kai sama da kashi 50 cikin 100 na wannan adadin kudi.

Da yake yin tsokaci kan kalubalen da ake fuskanta a fannin ya sanar da cewa, tsarin samar da rancen kudi na MPR da ke karkashin Babban Bankin Kasa (CBN), ya kara kudin ruwa na bayar da rancen kudin noma daga kashi 18 cikin 100 zuwa kashi 27 cikin 100, inda ya sanar da cewa; wannan babban kalubale ne ga wadanda suke fannin na renon tsirran.

Kazalika, ya sanar da cewa, wani karin kalubalen da manoman da ke Arewacin kasar nan ke fusanta shi ne, na tsadar biyan Leburori.

“Akasarin Leburorinmu, bisa rahotannin da muke samu shi ne, suna zuwa ne daga wasu iyakokin kasar nan, sannan kuma ga yadda darajar Naira ta fadi, inda ya kara da cewa; a cikin shekaru biyu zuwa uku, ba mu ji da dadi ba; musamman ganin yadda darajar Naira ta fadi warwas, kan takardar CFA, wanda hakan ya sa biyan aikin da Leburorin suka yi ya karu”, in ji Idris.

Shi kuwa, a nasa jawabin a wajen taron Jakadan Kasar Netherlands a Nijeriya, Bengt ban Loosdrecht, ya bayyana cewa; fannin na renon tsirrai na taimakawa wajen kara bunkasa tattalin arzikin kasar da samar da aikin yi tare kuma da samar da abinci mai gina jiki.

Sai dai, Jakadan ya yi nuni da cewa; za a iya samun hakan ne, kawai idan aka samar da rancen kudade ga wadanda suke cikin fannin, wanda ita ce kadai mafita.

Bengt ban Loosdrecht, wanda Mista Folusho Adejoro, Mai Bayar da shawara a bangaren samar da wadataccen abinci da rage dumamar yanayi a ofishin Jakadancin kasar ta Netherlands a Nijeriya ya wakilce shi a wajen taron, ya bayyana cewa, manoma da dama a wannan fannin, na yin aiki tukuru, sai dai, suna fuskantar kalubalen samun rancen kudin renon na tsirrai.

Ya ci gaba da cewa, manufar taron shi ne, domin cike gibin da ake da shi na samar da damar samun rancen kudaden, wanda hakan zai bai wa bankuna da sauran cibiyoyin bayar da rancen kudaden noma fahimtar damar da ke cikin wannan fanni.

Ofishin Jakadanci na kasar ta Netherlands da ke kasar nan ce ke bayar da dauki a shirin habaka renonin tsirrai, wanda aka faro shirin tun a 2021 zuwa 2025, musaman domin tallafa wa fannin tare da samar da wadataccen abinci mai gina jiki a daukacin fadin Nijeriya baki-daya.

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.