• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

by Abubakar Abba
2 days ago
in Noma Da Kiwo
0
Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar bunkasa kiwo ta hanyar cibiyar gudanar da bincken kula da lafiyar dabbobi ta kasa (NAPRI) da ke garin Shika, a Qaramar Hukumar Zaria a Jihar Kaduna, ta gabatar wasu nau’ika takwas na ciyar da Shanu da aka yi wa rijista, bayan aminta da su a shekaru 48 kan daukin da aka samar.

Wannan na kunshe ne, cikin sanarwar da ma’aikatar ta fitar, inda ta bayyana cewa; yin rijistar da kuma fitar da wadannan nau’ika takwas na ciyarwar ciyar da Shanu, wata babbar nasara ce ga ma’aikatar, musamman ganin cewa; ita ce ta farko bayan shekaru 48.

  • Tsawa Ta Kashe Makiyayi Da Shanu A Kudancin Kaduna
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina

Sanarwar ta ce, nau’ikan ciyawar, an mika su ga kwamiti na kasa da ke lura da nau’ikan ciyawa, domin yi wa nau’ikan rijista, sannan kuma a fitar da su.

A cewar sanarwar, nau’ikan ciyawar takwas, sun cimma  matakin amincewa na cibiyar kula da jinsin ciyawa ta kasa, wato GRB da ke garin Ibadan, inda aka gabatarwa da cibiyar domin ta yi musu rijista a kuma fitar da nau’in ciyawar.

“Hakan ya kawo jimlar nau’ika guda dari na ciyawar da aka yi wa rijista a kasar, aka kuma fitar da su, musamman domin a kara bunkasa kiwon Shanu a kasar“, in ji Sanarwar.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

Sanarwar ta ci gaba da cewa; yi wa nau’ikan ciyawar takwas rijista da kuma fitar da su, wani sabon sauyi ne kan samar da ciyawar ciyar da Shanun ciki, har da tsarin samar da ingantaccen Irin noma da kuma kara habaka bangaren kiwon dabbobi a kasar.

A cewar sanawar, hakan kuma zai kara taimakawa a bangaren zuba hannun jarin samar da abincin dabbobi da kara bunkasa kasuwancin abincin dabbobi da kuma kara fitar da abincin nasu, zuwa kasar waje.

Kazalika, ma’aiktar ta bayyana cewa, yi wa nau’ikan ciyawar takwas rijista da kuma amincewa da su, hakan zai taimaka wajen tabbatar da kara samar da ingantaccen Irin noma tsaftatacce wanda kuma hakan zai taimaka wa manoman kasar da masu kiwon dabbobi da kuma samar da kyakkyawan yanayi.

“Ingantaccen Irin noman da aka amince da shi ya kasance mai saurin nuna idan an shuka shi, wanda kuma ke jurewa dukkanin wani nau’ikan cututtukan da ke lalata Irin noma“, a cewar sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa, hakan zai kuma kara taimakawa wajen kara samar da lafiyar ciyarwar, musamman wadda za ta taimaka wajen kara habaka kiwon dabbobi a dukkanin fadin wannan kasa.

Sanawar ta bayyana cewa, wannan amincewar da aka yi da Irin na noma, ya kai matsayin da ake bukata a hukumance, musamman domin tabbatar da an samar da zabin nau’ikan Irin noman da ake bukata.

A cewar sanarwar, hakan zai kuma taimaka matuka wajen kaucewa yin asara, sakamakon harbin cututtukan da ke kara habaka kasuwa da kara bunkasa zuba hannun jari da kare muhalli da sauran makamantansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TarayyaShahu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Next Post

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Related

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

3 days ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

3 days ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

4 days ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

1 week ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

1 week ago
Sin Ta Gina Cibiyoyin Fasahar Aikin Gona Na Gwaji Guda 24 A Afirka
Noma Da Kiwo

Muhimman Dalilan Kirkiro Da Shirin Inganta Aikin Noma ‘SAPZ’

2 weeks ago
Next Post
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

May 12, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

May 12, 2025
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

May 12, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

May 12, 2025
Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

May 12, 2025
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

May 12, 2025
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

May 12, 2025
Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 12, 2025
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

May 12, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.