• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

by Abubakar Abba
5 months ago
Shanu

Ma’aikatar bunkasa kiwo ta hanyar cibiyar gudanar da bincken kula da lafiyar dabbobi ta kasa (NAPRI) da ke garin Shika, a Qaramar Hukumar Zaria a Jihar Kaduna, ta gabatar wasu nau’ika takwas na ciyar da Shanu da aka yi wa rijista, bayan aminta da su a shekaru 48 kan daukin da aka samar.

Wannan na kunshe ne, cikin sanarwar da ma’aikatar ta fitar, inda ta bayyana cewa; yin rijistar da kuma fitar da wadannan nau’ika takwas na ciyarwar ciyar da Shanu, wata babbar nasara ce ga ma’aikatar, musamman ganin cewa; ita ce ta farko bayan shekaru 48.

  • Tsawa Ta Kashe Makiyayi Da Shanu A Kudancin Kaduna
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina

Sanarwar ta ce, nau’ikan ciyawar, an mika su ga kwamiti na kasa da ke lura da nau’ikan ciyawa, domin yi wa nau’ikan rijista, sannan kuma a fitar da su.

A cewar sanarwar, nau’ikan ciyawar takwas, sun cimma  matakin amincewa na cibiyar kula da jinsin ciyawa ta kasa, wato GRB da ke garin Ibadan, inda aka gabatarwa da cibiyar domin ta yi musu rijista a kuma fitar da nau’in ciyawar.

“Hakan ya kawo jimlar nau’ika guda dari na ciyawar da aka yi wa rijista a kasar, aka kuma fitar da su, musamman domin a kara bunkasa kiwon Shanu a kasar“, in ji Sanarwar.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Sanarwar ta ci gaba da cewa; yi wa nau’ikan ciyawar takwas rijista da kuma fitar da su, wani sabon sauyi ne kan samar da ciyawar ciyar da Shanun ciki, har da tsarin samar da ingantaccen Irin noma da kuma kara habaka bangaren kiwon dabbobi a kasar.

A cewar sanawar, hakan kuma zai kara taimakawa a bangaren zuba hannun jarin samar da abincin dabbobi da kara bunkasa kasuwancin abincin dabbobi da kuma kara fitar da abincin nasu, zuwa kasar waje.

Kazalika, ma’aiktar ta bayyana cewa, yi wa nau’ikan ciyawar takwas rijista da kuma amincewa da su, hakan zai taimaka wajen tabbatar da kara samar da ingantaccen Irin noma tsaftatacce wanda kuma hakan zai taimaka wa manoman kasar da masu kiwon dabbobi da kuma samar da kyakkyawan yanayi.

“Ingantaccen Irin noman da aka amince da shi ya kasance mai saurin nuna idan an shuka shi, wanda kuma ke jurewa dukkanin wani nau’ikan cututtukan da ke lalata Irin noma“, a cewar sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa, hakan zai kuma kara taimakawa wajen kara samar da lafiyar ciyarwar, musamman wadda za ta taimaka wajen kara habaka kiwon dabbobi a dukkanin fadin wannan kasa.

Sanawar ta bayyana cewa, wannan amincewar da aka yi da Irin na noma, ya kai matsayin da ake bukata a hukumance, musamman domin tabbatar da an samar da zabin nau’ikan Irin noman da ake bukata.

A cewar sanarwar, hakan zai kuma taimaka matuka wajen kaucewa yin asara, sakamakon harbin cututtukan da ke kara habaka kasuwa da kara bunkasa zuba hannun jari da kare muhalli da sauran makamantansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.