• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Daina Ciyar Da Fursunoni Abinci

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Za Ta Daina Ciyar Da Fursunoni Abinci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya za ta dakatar da ciyar da sama da fursunoni 75,507 da ke gidajen yari 244 a kasar nan daga ranar 31 ga watan Disamban 2023 yayin da gwamnatin jihohi kuma ake tsammanin za su fara ciyar da masu laifin a jihohinsu kai tsaye.

Ministan kula da harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, shi ne ya shelanta hakan a jiya sa’ilin da ke kaddamar da shalkwatar hukumar kula da gidajen yari (NCoS) a Owerri da ke Jihar Imo.

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutumin Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa
  • Gawar Wani Tsoho Mai Shekara 115 Ta Yi Batan Dabo A Anambra

Aregbesola, ya ce, kashi 90 cikin 100 na fursunonin da ake da su, mutane ne da suka yi laifi wa jiharsu, don haka lokaci ya yi da jihohi za su fara zuba kudade su na ciyar da masu laifinsu.

Wannan bayanin na zuwa ne kasa da awa 24 da gwamnatin tarayya ta fito ta ce, tana kashe naira biliyan N22.4 wajen ciyar da fursunoni a fadin kasar nan, kuma har an shigar da hakan cikin kasafin kudin 2023.

Ya hakikance kan cewa matakin zai taimaka wajen rage cinkoson fursunoni a gidajen yarin kasar nan, Aregbesola ya na mai karawa da cewa kaso 80 na fursunoni su na zaman jiran shari’a ne.

Labarai Masu Nasaba

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

Ya ce, akwai bukatar a sake waiwaye sosai kan tsarin shari’a a fadin kasar nan ta yadda za a ke yanke wa masu jiran shari’a hukunci a kan lokaci da daure wadanda suka dace.

A fadinsa, gwamnatin shugaba Buhari ta yi kokari sosai wajen gyara tsare-tsaren tafiyar da gidajen yari ta hanyar kara kudin da ake kashewa, kwaskwarima wa gidajen yari da kuma gina wasu sabbi dukka a kokarin rage yawan cunkoso.

Ministan ya kara da cewa, “Babban kalubalenmu shi ne yawan cinkoson fursunoni a gidajen yari, musamman a biranen da ke da yawan jama’a da yadda mu’amalar jama’a ke karuwa, don haka aikata laifuka zai karu a wannan wajen don haka ne sai ta kai an ajiye wasu a gidajen yari.

“Mun yi kokarin shawo kan wannan matsalar ta hanyar gina manyan gidajen yari guda shida a shiyyoyi shida da suke fadin kasar nan. Na Kano da na Abuja tunin aka kammala su, sauran ma za a kammala.”

Ya nanata cewa akwai gayar bukatar gyara kan tsarin shari’a ta yadda za a yi waiwaye ga dukkanin abubuwan da suke haifar da jinkirin shari’a domin a cewarsa kaso 70 zuwa ma 80 suna zaman jiran shari’a wanda hakan ba daidai ba ne, “Domin na tabbata a wasu lokutan ana tsare wadanda ma basu da laifi a yi ta ajiyesu a gidajen yari, ta hanyar gudanar da shari’a cikin hanzari ne za a gano mai laifi a yanke masa hukunci wanda bai da laifi a sake shi.”

“Wasu kuma koda sun yi laifin, hukuncin da za a yanke musu bai wuce watanni shida ba ya danganta da laifukan da suka aikata. To amma idan ba a yi shari’a ba sai mutum ya shafe tsawon lokaci a tsare.”

“Jihohi su tashi tsaye su gyara sashin shari’arsu su tabbatar ana yanke hukunci a kan lokaci da hanzarin yin shari’a. Wannan zai taimaka sosai wajen wanzar da adalci da kuma kawo karshen zare wanda ake zargi in ya yi laifi kuma a hukunta shi, in bai yi ba a sake shi,” ya shaida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbinciAregbesolaFursunoni
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Kama Mutumin Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

Next Post

Rayuwar Amina Muhammad, Mataimakiyar Sakatare-Janar Na Majalisar Dinkin Duniya A Takaice

Related

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Tsaro

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

2 hours ago
Kotu
Tsaro

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

2 hours ago
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4
Tsaro

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

3 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

5 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

17 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

18 hours ago
Next Post
Rayuwar Amina Muhammad, Mataimakiyar Sakatare-Janar Na Majalisar Dinkin Duniya A Takaice

Rayuwar Amina Muhammad, Mataimakiyar Sakatare-Janar Na Majalisar Dinkin Duniya A Takaice

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.