Gwamnatin Jihar Yobe ta sanar da rufe dukkanin makarantun gwamnati da masu zaman kansu a faɗin jihar na tsawon kwanaki 10 domin bai wa ɗalibai da malamai damar gudanar da bikin babbar sallah.
Ranar hutun za ta fara ne daga ranar Laraba, 4 ga watan Yuni, 2025, zuwa Lahadi, 15 ga Yuni, 2025, kamar yadda wata sanarwa da Daraktan Kula da Makarantu, Bukar Modu, ya sanya wa hannu a madadin Kwamishinan Ilimin jihar.
- An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana
- Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya
Hutun ya yi daidai da sanarwar Majalisar Manyan Malaman Addinin Musulunci ta Nijeriya da ta ayyana Juma’a, 7 ga watan Yuni, 2025, a matsayin ranar Sallah, tare da ranar Dimokuraɗiyya da za a yi a ranar Laraba, 12 ga watan Yuni, 2025.
Ma’aikatar Ilimi ta umarci dukkanin makarantun da su kasance a rufe a wannan lokaci domin bai wa ɗalibai, malamai da iyaye damar yin bukukuwan cikin natsuwa.
Kwamishinan Ilimi na jihar, Farfesa Adam Idris, ya yi wa kowa fatan alheri da zaman lafiya a lokacin bukukuwan babbar sallah, tare da kira ga iyaye da su kula da ’ya’yansu a lokacin da bayan Sallah.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp