• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Yobe Ta Sanya Wa Kasuwar Nguru Sunan Shehu Gibrima

by Muhammad Maitela
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Yobe Ta Sanya Wa Kasuwar Nguru Sunan Shehu Gibrima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Yobe, bisa jagorancin Hon. Mai Mala Buni ta sanya wa sabuwar kasuwar da ta kammala ginawa a garin Nguru a jihar (Nguru International Modern Market), sunan Shehun Malamin addinin musuluncin nan Shehu Muhammad Gibirima.

A sanarwar manema labaru, mai dauke da sa-hannun Darakta-Janar kan hulda da ‘yan jaridu da kafafen yada labarai a ofishin Gwamnan, Alhaji Mamman Mohammed, da yammacin ranar Alhamis, Gwamnan ya sanar da hakan ne a lokacin da ya karbi bakoncin Malama Aisha AbdulMutalib, ‘yar asalin garin Potiskum, wadda da ta yi nasarar zama gwarzuwa a gasar karatun Alkur’anin Mai Tsarki (rukunin mata) a garin Gusau ta jihar Zamfara.

  • Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Gwamna Buni ya bayyana cewa ya sanya wa kasuwar sunan Shehin Malamin ne domin tunawa da gagarumar gudummawar da ya bayar wajen yada addinin musulunci a wannan nahiyar.

“Sannan kuma a matsayin sa na Malamin Addinin musulunci a fadin duniya, wanda al’ummar musulmin duniya ke girmamawa, bisa gudumawar da ya bayar.” In ji Buni.

Dangane da gwarzuwar gasar Alkur’anin kuwa, Gwamna Buni ya bayyana jindadinsa dangane da kokarin Malama Aisha, inda ya nunata a matsayin abin alfahari ga jihar Yobe.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Gibrima
Gwarzuwar gasar Alkur’anin bangaren mata, Malama Aisha

 

Sakamakon haka, Gwamna Buni ya gwangwaje Hafiza Aisha da kyautar gida, kuma ya nadata a matsayin mai bashi shawara kan harkokin abubuwan da suka shafi haddar Alqura’ni Mai Tsarki, tallafin gurbin karatu da kujerar aikin Hajji tare da mijinta.

Har ila yau kuma, Gwamnan ya bai wa dukan yan kwamitin da suka jagoranci gasar karatun Alkur’anin zuwa samun wannan nasarar kyautar kujerun aikin Hajjin bana.

Alhaji Mamman Mohammed ya kara da cewa, Gwamna Buni ya jaddada ribanya kokarin gwamnatinsa wajen samar da ingantaccen ilimin addinin musulunci da na boko a jihar.

Gwamna Buni ya kara da cewa, kuma a matsayin jihar Yobe a cikin tsohuwar Daular Ngazargamo wadda aka santa da hidima tare da yada ilimin addinin musulunci, wannan zai ci gaba da kasancewa a zahiri wajen tanadar kyakkyawan sunan da aka san Daular da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Sace 89trn: Dan Takara A Kano Zai Maka Buhari A Kotu

Next Post

Wasu Jiga-jigan APC Da Ba A Jin Duriyarsu A Yakin Neman Zaben Tinubu

Related

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

3 minutes ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

2 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

17 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

17 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

18 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

18 hours ago
Next Post
Tarihin Zaben 1993 Zai Maimaitu, Jama’ar Kano Za Su Yi Watsi Da Kwankwaso Su Dauki Tinubu – Ganduje

Wasu Jiga-jigan APC Da Ba A Jin Duriyarsu A Yakin Neman Zaben Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.