• English
  • Business News
Saturday, May 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Yobe Ta Sanya Wa Kasuwar Nguru Sunan Shehu Gibrima

by Muhammad Maitela
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Yobe Ta Sanya Wa Kasuwar Nguru Sunan Shehu Gibrima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Yobe, bisa jagorancin Hon. Mai Mala Buni ta sanya wa sabuwar kasuwar da ta kammala ginawa a garin Nguru a jihar (Nguru International Modern Market), sunan Shehun Malamin addinin musuluncin nan Shehu Muhammad Gibirima.

A sanarwar manema labaru, mai dauke da sa-hannun Darakta-Janar kan hulda da ‘yan jaridu da kafafen yada labarai a ofishin Gwamnan, Alhaji Mamman Mohammed, da yammacin ranar Alhamis, Gwamnan ya sanar da hakan ne a lokacin da ya karbi bakoncin Malama Aisha AbdulMutalib, ‘yar asalin garin Potiskum, wadda da ta yi nasarar zama gwarzuwa a gasar karatun Alkur’anin Mai Tsarki (rukunin mata) a garin Gusau ta jihar Zamfara.

  • Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Gwamna Buni ya bayyana cewa ya sanya wa kasuwar sunan Shehin Malamin ne domin tunawa da gagarumar gudummawar da ya bayar wajen yada addinin musulunci a wannan nahiyar.

“Sannan kuma a matsayin sa na Malamin Addinin musulunci a fadin duniya, wanda al’ummar musulmin duniya ke girmamawa, bisa gudumawar da ya bayar.” In ji Buni.

Dangane da gwarzuwar gasar Alkur’anin kuwa, Gwamna Buni ya bayyana jindadinsa dangane da kokarin Malama Aisha, inda ya nunata a matsayin abin alfahari ga jihar Yobe.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

Gibrima
Gwarzuwar gasar Alkur’anin bangaren mata, Malama Aisha

 

Sakamakon haka, Gwamna Buni ya gwangwaje Hafiza Aisha da kyautar gida, kuma ya nadata a matsayin mai bashi shawara kan harkokin abubuwan da suka shafi haddar Alqura’ni Mai Tsarki, tallafin gurbin karatu da kujerar aikin Hajji tare da mijinta.

Har ila yau kuma, Gwamnan ya bai wa dukan yan kwamitin da suka jagoranci gasar karatun Alkur’anin zuwa samun wannan nasarar kyautar kujerun aikin Hajjin bana.

Alhaji Mamman Mohammed ya kara da cewa, Gwamna Buni ya jaddada ribanya kokarin gwamnatinsa wajen samar da ingantaccen ilimin addinin musulunci da na boko a jihar.

Gwamna Buni ya kara da cewa, kuma a matsayin jihar Yobe a cikin tsohuwar Daular Ngazargamo wadda aka santa da hidima tare da yada ilimin addinin musulunci, wannan zai ci gaba da kasancewa a zahiri wajen tanadar kyakkyawan sunan da aka san Daular da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Sace 89trn: Dan Takara A Kano Zai Maka Buhari A Kotu

Next Post

Wasu Jiga-jigan APC Da Ba A Jin Duriyarsu A Yakin Neman Zaben Tinubu

Related

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya

31 minutes ago
Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

9 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

12 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

12 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 2, Sun Kwato Shanu 1,000 A Taraba
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 2, Sun Kwato Shanu 1,000 A Taraba

15 hours ago
Minista Ya Ƙaryata Jita-jitar Mayar Da Taron Bayanin Ministoci Zuwa London
Labarai

Minista Ya Ƙaryata Jita-jitar Mayar Da Taron Bayanin Ministoci Zuwa London

15 hours ago
Next Post
Tarihin Zaben 1993 Zai Maimaitu, Jama’ar Kano Za Su Yi Watsi Da Kwankwaso Su Dauki Tinubu – Ganduje

Wasu Jiga-jigan APC Da Ba A Jin Duriyarsu A Yakin Neman Zaben Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya

May 17, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

May 16, 2025
Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

May 16, 2025
JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

May 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

May 16, 2025
CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

May 16, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

May 16, 2025
Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

May 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.