• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Yobe Ta Sanya Wa Kasuwar Nguru Sunan Shehu Gibrima

by Muhammad Maitela
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Yobe Ta Sanya Wa Kasuwar Nguru Sunan Shehu Gibrima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Yobe, bisa jagorancin Hon. Mai Mala Buni ta sanya wa sabuwar kasuwar da ta kammala ginawa a garin Nguru a jihar (Nguru International Modern Market), sunan Shehun Malamin addinin musuluncin nan Shehu Muhammad Gibirima.

A sanarwar manema labaru, mai dauke da sa-hannun Darakta-Janar kan hulda da ‘yan jaridu da kafafen yada labarai a ofishin Gwamnan, Alhaji Mamman Mohammed, da yammacin ranar Alhamis, Gwamnan ya sanar da hakan ne a lokacin da ya karbi bakoncin Malama Aisha AbdulMutalib, ‘yar asalin garin Potiskum, wadda da ta yi nasarar zama gwarzuwa a gasar karatun Alkur’anin Mai Tsarki (rukunin mata) a garin Gusau ta jihar Zamfara.

  • Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Gwamna Buni ya bayyana cewa ya sanya wa kasuwar sunan Shehin Malamin ne domin tunawa da gagarumar gudummawar da ya bayar wajen yada addinin musulunci a wannan nahiyar.

“Sannan kuma a matsayin sa na Malamin Addinin musulunci a fadin duniya, wanda al’ummar musulmin duniya ke girmamawa, bisa gudumawar da ya bayar.” In ji Buni.

Dangane da gwarzuwar gasar Alkur’anin kuwa, Gwamna Buni ya bayyana jindadinsa dangane da kokarin Malama Aisha, inda ya nunata a matsayin abin alfahari ga jihar Yobe.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

Gibrima
Gwarzuwar gasar Alkur’anin bangaren mata, Malama Aisha

 

Sakamakon haka, Gwamna Buni ya gwangwaje Hafiza Aisha da kyautar gida, kuma ya nadata a matsayin mai bashi shawara kan harkokin abubuwan da suka shafi haddar Alqura’ni Mai Tsarki, tallafin gurbin karatu da kujerar aikin Hajji tare da mijinta.

Har ila yau kuma, Gwamnan ya bai wa dukan yan kwamitin da suka jagoranci gasar karatun Alkur’anin zuwa samun wannan nasarar kyautar kujerun aikin Hajjin bana.

Alhaji Mamman Mohammed ya kara da cewa, Gwamna Buni ya jaddada ribanya kokarin gwamnatinsa wajen samar da ingantaccen ilimin addinin musulunci da na boko a jihar.

Gwamna Buni ya kara da cewa, kuma a matsayin jihar Yobe a cikin tsohuwar Daular Ngazargamo wadda aka santa da hidima tare da yada ilimin addinin musulunci, wannan zai ci gaba da kasancewa a zahiri wajen tanadar kyakkyawan sunan da aka san Daular da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Sace 89trn: Dan Takara A Kano Zai Maka Buhari A Kotu

Next Post

Wasu Jiga-jigan APC Da Ba A Jin Duriyarsu A Yakin Neman Zaben Tinubu

Related

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

3 hours ago
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
Labarai

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

4 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

6 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

6 hours ago
EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi
Labarai

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

7 hours ago
Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
Labarai

Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Tarihin Zaben 1993 Zai Maimaitu, Jama’ar Kano Za Su Yi Watsi Da Kwankwaso Su Dauki Tinubu – Ganduje

Wasu Jiga-jigan APC Da Ba A Jin Duriyarsu A Yakin Neman Zaben Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.