• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

by Abubakar Sulaiman
1 week ago
in Ilimi
0
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni, ya amince da shirya babban taron girmamawa ga Nafisa Abdullah Aminu, ’yar shekara 17 da ta zama zaƙaƙurar duniya a fannin ƙwarewar Turanci a gasar TeenEagle Global Finals 2025 da aka gudanar a birnin London,da ke ƙasar Ingila.

Nafisa, ɗalibar makarantar Nigerian Tulip International College (NTIC), ta doke fiye da mutane 20,000 daga ƙasashe 69, ciki har da ƙasashen da ke amfani da Turanci a matsayin harshen uwa, lamarin da ya ja hankalin duniya ga ilimin Nijeriya.

  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
  • Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Gwamna Buni ya bayyana nasarar Nafisa a matsayin wata babbar girmamawa ga jihar Yobe da Nijeriya baki ɗaya, yana mai cewa wannan nasara sakamako ne na zuba jari da gwamnatin sa ke yi a fannin ilimi.

 

A cewar sanarwar da Mamman Mohammed, Daraktan yaɗa labarai na Gwamnan ya fitar, Nafisa na daga cikin ɗaliban da ke amfana da tallafin karatu daga gwamnatin jihar Yobe, wadda ta riga ta tallafa wa sama da ɗalibai 40,000 a matakin jami’a da sauran manyan makarantu a cikin gida da waje.

Labarai Masu Nasaba

Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

Gwamnan ya bayyana cewa za a gudanar da babban taron girmamawa ga Nafisa a faɗin jihar, sannan ya sake jaddada ƙudirin gwamnatinsa na ci gaba da gyaran makarantu da ɗaukar malamai domin ganin kowanne yaro a Yobe ya samu ingantaccen ilimi kamar Nafisa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EnglishYobe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

Next Post

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

Related

Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya
Ilimi

Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya

2 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

3 weeks ago
‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato
Ilimi

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

4 weeks ago
UTME
Ilimi

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

4 weeks ago
Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50
Ilimi

Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

4 weeks ago
Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano
Ilimi

Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

4 weeks ago
Next Post
Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao

PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao

August 13, 2025
NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

August 13, 2025
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

August 13, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.