• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Da Ba Za Su Iya Biyan Mafi Ƙarancin Albashin Naira 70,000 A Nijeriya

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnonin Da Ba Za Su Iya Biyan Mafi Ƙarancin Albashin Naira 70,000 A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan da Shugaba Bola Tinubu ya gabatar da sabon mafi karancin albashi na Naira 70,000, wasu gwamnonin jihohin Nijeriya, sun bayyana cewa ba za su iya biyan wannan sabon albashin ba saboda matsalolin kudi. 

Ga jerin gwamnonin:

  • Lokuta Da Yawa Nakan Dakata In Yi Kuka Ma’ishi Kafin Na Ci Gaba Da Rubutu – Fatima Gurin
  • Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu

Jihar Gombe: Gwamna Inuwa Yahaya

Gwamna Inuwa Yahaya na Jihar Gombe, ya ce gwamnatinsa ba za ta iya biyan sabon albashin Naira 70,000 ba saboda kudaden da jihar ke samu daga gwamnatin tarayya ba za su isa ba.

Yahaya, wanda kuma shi ne shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa, ya ce biyan tsohon mafi karancin albashi na Naira 30,000 yana yi musu wahala.

Labarai Masu Nasaba

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Ya bayyana cewa da yawa daga cikin jihohi ba za su iya biyan karin albashin ba, duk da karin kudaden da suka samu daga gwamnatin tarayya a kwanan nan.

Jihar Nasarawa: Gwamna Abdullahi Sule

Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa, ya yanke shawarar jinkirta aiwatar da sabon tsarin mafi albashi na Naira 70,000 har zuwa shekarar 2026.

A baya, ya yi alkawarin fara biyan sabon albashin a wannan watan, tare da biyan bashin watannin da suka wuce.

Duk da haka, ya bayyana cewa jihar na bukatar kimanin Naira miliyan 200 domin biyan ma’aikata, wanda ya ce hakan ba zai yiwuwa jihar ta fara biyan sabon albashin a yanzu ba

Jihar Kogi: Gwamna Ahmed Usman Ododo

Gwamna Ahmed Usman Ododo na Jihar Kogi bai yanke shawara kan ko yaushe gwamnatinsa za ta fara biyan sabon mafi karancin Naira na 70,000 ba.

Kwamishinan kudi na jihar, Ashiwaju Ashiru Idris, ya ce ba a sanya ranar fara biyan sabon albashin ba.

Damuwar Masana’antu Masu Zaman Kansu

Kungiyar Masana’antu Masu Zaman Kansu (OPS), ita ma ta bayyana damuwa kan sabon albashin na Naira 70,000.

Sun ce zai yi wahala kamfanoni su iya biyan wannan sabon albashi ba tare da samun taimako na musamman ba.

Adewale-Smatt Oyerinde, mai magana da yawun Kungiyar Masu Daukar Ma’aikata ta Nijeriya (NECA), ya nuna damuwa kan yadda sabon tsari albashin zai jefa kamfanoni cikin matsalar kudi.

Martanin Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC)

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC) a Jihar Legas, ta fayyace cewa mafi karancin albashin Naira 35,000 da ake biya a halin yanzu daban ne da sabon mafi karancin albashi na Naira 70,000 da mayar doka kwana nan.

Funmi Sessi, shugaban NLC na Jihar Legas, ya yi kira da a samar da tsarin albashin da ya dace da nau’ikan ayyuka da matakan albashi daban-daban.

Wannan yanayin ya bayyana matsalolin kudi da jihohi da masana’antu daban-daban ke fuskanta wajen kokarin gyara tsarin albashinsu zuwa sabon mafi karancin albashi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GwamnoniLabaraiMa'aikataMafi Karancin Albashi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Lokuta Da Yawa Nakan Dakata In Yi Kuka Ma’ishi Kafin Na Ci Gaba Da Rubutu – Fatima Gurin

Next Post

Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Sin Da Laos Da Myanmar Da Thailand Sun Gudanar Da Wani Taro

Related

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe
Labarai

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

1 hour ago
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

3 hours ago
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

12 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

13 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

13 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

14 hours ago
Next Post
Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Sin Da Laos Da Myanmar Da Thailand Sun Gudanar Da Wani Taro

Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Sin Da Laos Da Myanmar Da Thailand Sun Gudanar Da Wani Taro

LABARAI MASU NASABA

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.