• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gyaran Kundin Tsarin Mulki: Ba Za Mu Taba Cin Amanar ‘Yan Nijeriya Ba -Majalisa

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
majalisar kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar wakilan Nijeriya ta bayyana cewa tana da kwarin giwa kan mataimakin shugaban majalisa, Rt. Hon. Benjamin Kalu, zai sauke nauyin da aka dora masa na shugabancin kwamitin gyaran kundin tsarin mulki, wanda ba za su taba cin amanan ‘yan Nijeriya ba.  

A kwanan nan ne majalisar ta kafa kwamiti da zai duba shawarwari na canje-canje da gyare-gyare na kundin tsarin mulki na shekarar 1999, inda aka dora shugabancin kwamitin ga Kalu tare da wasu kwararrun ‘yan majalisa a matsayin mambobi.

  • Ku Je Ku Magance Matsalar Yunwa Da Ta Addabi Jama’a -Fintiri
  • Babu Inda Na Ce Na Fi ‘Yan Nijeriya Shan Wahalar Tsadar Rayuwa -Ɗangote

Wannan kwamiti shi ne na shida da aka kafa tun a shekarar 1999, domin sake duba kundin tsarin mulki da ake amfani da shi a yanzu, ana tsammanin za a kaddamar da shi a ranar 26 ga Fabrairun 2024.

Da yake yi wa ‘yan jarida karin haske a Jihar Kano, mai magana da yawun mataimakin shugaban majalisar wakilai, Hon. Philip Agbese ya bayyana cewa ‘yan majalisa suna da kwarin gwiwa a kan mataimakin shugaban majalisar wakilai, kuwa kwamitinsa zai yi aikin da aka dora masa kan lokaci.

Ya ce, “Tun lokaci mai tsawo majalisar kasa take yunkurin sake fasalin kundin tsarin mulki na shekarar 1999, tare da niyyar sauya wasu daga cikin dokokin ta yadda za su dace da zamani. A wasu lokutan, majalisa na samun nasara, amma kuma a wani sa’ilin kwamitin majalisa yakan gaza yin aikinsa.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

“Amma wannan kwamitin da aka danka wa Rt. Hon. Benjamin Kalu zai samu nasarar yin aikin gyara kundin tsarin mulkin kasar nan. Ya kamata ‘yan Nijeriya su kwantar da hankalinsu a rana daya komai zai iya sauyawa.

“Wannan kwamitin zai yi amfani da shawarwarin mutane da mabambantan masu ruwa da tsaki da kungiyoyin fararen hula da ma’aikatun gwamnati da masarautun gargajiya da kungiyoyin mata da kuma ‘yan kasuwa masu zaman kansu wadanda suke taimakawa wajen bunkasa tattalin arziki, domin samun nasarar gyarar kundin tsarin mulkin Nijeriya.”

Haka kuma Hon. Agbese ya bayyana cewa wannan lokaci ne da kungiyoyi da ma’aikatun gwamnati za su samu dama na sauya wasu daga cikin dokokin tsarin mulki na 1999, domin yin aiki kafada da kafada da wakilansu a lokacin da kwamitin ya fara aiki a hukumanci a kasrshen wannan wata.

“Akwai kudurorin doka guda 40 da majalisa ke neman a saka su a cikin tsarin mulki. Wasu daga ciki za su kawo karshen matsalolin jinsi da masarautun gargajiya da bai wa kananan hukumomin ‘yancin gashin kai da matsalolin kudade da dai sauransu.

“Kwamitin zai tabbatar ya kammala aikinsa a watan Disambar 2025. Ina kira ga masu ruwa da tsaki da su yi aiki kafada da kafada da wakilolinsu da kwamitin saboda a kammala aikin kan lokaci.”

Mataimakin shugaban majalisar wakilai kuma shugaban kwamitin gyaran kundin tsarin mulki ya gana da dukkan mambobin kwamitin a ranar Laraba da ta gabata, inda ya yi alkawarin cewa kwamitin zai kammala aikinsa a watan Disambar 2025.

Kalu ya bukaci mambobin kwamitin da su shirya yin aiki tukuru saboda samun damar yi sauye-sauye na kundin tsarin mulki kan lokaci kamar yadda suka yi wa ‘yan Nijeriya alkawari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin Tarayyamajalisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sake Yoyon Gurbatacciyar Ruwan Nukiliya Ta Fukushima Ya Aika Sako Ga Japan

Next Post

Murnar Bikin Bazara Na Kasar Sin Ya Haskaka Gasar Wasan Kwallon Gora Kan Kankara Ta Arewacin Amurka

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

19 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Majalisa
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
bikin bazara

Murnar Bikin Bazara Na Kasar Sin Ya Haskaka Gasar Wasan Kwallon Gora Kan Kankara Ta Arewacin Amurka

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.