• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gyaran Kundin Tsarin Mulki: Ba Za Mu Taba Cin Amanar ‘Yan Nijeriya Ba -Majalisa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
majalisar kasa

Majalisar wakilan Nijeriya ta bayyana cewa tana da kwarin giwa kan mataimakin shugaban majalisa, Rt. Hon. Benjamin Kalu, zai sauke nauyin da aka dora masa na shugabancin kwamitin gyaran kundin tsarin mulki, wanda ba za su taba cin amanan ‘yan Nijeriya ba.  

A kwanan nan ne majalisar ta kafa kwamiti da zai duba shawarwari na canje-canje da gyare-gyare na kundin tsarin mulki na shekarar 1999, inda aka dora shugabancin kwamitin ga Kalu tare da wasu kwararrun ‘yan majalisa a matsayin mambobi.

  • Ku Je Ku Magance Matsalar Yunwa Da Ta Addabi Jama’a -Fintiri
  • Babu Inda Na Ce Na Fi ‘Yan Nijeriya Shan Wahalar Tsadar Rayuwa -Ɗangote

Wannan kwamiti shi ne na shida da aka kafa tun a shekarar 1999, domin sake duba kundin tsarin mulki da ake amfani da shi a yanzu, ana tsammanin za a kaddamar da shi a ranar 26 ga Fabrairun 2024.

Da yake yi wa ‘yan jarida karin haske a Jihar Kano, mai magana da yawun mataimakin shugaban majalisar wakilai, Hon. Philip Agbese ya bayyana cewa ‘yan majalisa suna da kwarin gwiwa a kan mataimakin shugaban majalisar wakilai, kuwa kwamitinsa zai yi aikin da aka dora masa kan lokaci.

Ya ce, “Tun lokaci mai tsawo majalisar kasa take yunkurin sake fasalin kundin tsarin mulki na shekarar 1999, tare da niyyar sauya wasu daga cikin dokokin ta yadda za su dace da zamani. A wasu lokutan, majalisa na samun nasara, amma kuma a wani sa’ilin kwamitin majalisa yakan gaza yin aikinsa.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

“Amma wannan kwamitin da aka danka wa Rt. Hon. Benjamin Kalu zai samu nasarar yin aikin gyara kundin tsarin mulkin kasar nan. Ya kamata ‘yan Nijeriya su kwantar da hankalinsu a rana daya komai zai iya sauyawa.

“Wannan kwamitin zai yi amfani da shawarwarin mutane da mabambantan masu ruwa da tsaki da kungiyoyin fararen hula da ma’aikatun gwamnati da masarautun gargajiya da kungiyoyin mata da kuma ‘yan kasuwa masu zaman kansu wadanda suke taimakawa wajen bunkasa tattalin arziki, domin samun nasarar gyarar kundin tsarin mulkin Nijeriya.”

Haka kuma Hon. Agbese ya bayyana cewa wannan lokaci ne da kungiyoyi da ma’aikatun gwamnati za su samu dama na sauya wasu daga cikin dokokin tsarin mulki na 1999, domin yin aiki kafada da kafada da wakilansu a lokacin da kwamitin ya fara aiki a hukumanci a kasrshen wannan wata.

“Akwai kudurorin doka guda 40 da majalisa ke neman a saka su a cikin tsarin mulki. Wasu daga ciki za su kawo karshen matsalolin jinsi da masarautun gargajiya da bai wa kananan hukumomin ‘yancin gashin kai da matsalolin kudade da dai sauransu.

“Kwamitin zai tabbatar ya kammala aikinsa a watan Disambar 2025. Ina kira ga masu ruwa da tsaki da su yi aiki kafada da kafada da wakilolinsu da kwamitin saboda a kammala aikin kan lokaci.”

Mataimakin shugaban majalisar wakilai kuma shugaban kwamitin gyaran kundin tsarin mulki ya gana da dukkan mambobin kwamitin a ranar Laraba da ta gabata, inda ya yi alkawarin cewa kwamitin zai kammala aikinsa a watan Disambar 2025.

Kalu ya bukaci mambobin kwamitin da su shirya yin aiki tukuru saboda samun damar yi sauye-sauye na kundin tsarin mulki kan lokaci kamar yadda suka yi wa ‘yan Nijeriya alkawari.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
bikin bazara

Murnar Bikin Bazara Na Kasar Sin Ya Haskaka Gasar Wasan Kwallon Gora Kan Kankara Ta Arewacin Amurka

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

October 24, 2025
Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu

Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu

October 24, 2025
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu

Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

October 24, 2025
Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.