• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Zai Bunkasa Ayyukan Masana’antu A Afrika

by CMG Hausa
2 years ago
Kasar Sin

Mataimakin ministan kula da cinikayya da masana’antu na kasar Ghana, Michael Okyere Baafi, ya ce ya kamata kasashen Afrika su dauki taron baje kolin tattalin arziki da cinikayya na Sin da Afrika karo na 3 a matsayin wata dama ta karfafa hadin gwiwa da kasar Sin domin bunkasa raya masana’antu da ababen more rayuwa.

Micheal Baafi ya bayyana haka ne ga kamfanin dillancin labarai na Xinhua yayin wani taro jiya, domin yayata baje kolin tattalin arziki da cinikayya na Sin da Afrika karo na 3.

  • Xi Ya Amsa Wasikar Daliban Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya

Baje kolin mai taken “ci gaba na bai daya domin makoma ta bai daya”, zai gudana ne daga ranar 29 ga watan Yuni zuwa 2 ga watan Yuli a Changsha, babban birnin lardin Hunan na tsakiyar kasar Sin.

Yayin taron da ya gudana a birnin Accra na Ghana, jami’an kasar Sin sun gabatar da manufofin zuba jari masu gwabi ga ‘yan kasuwar kasar, da fatan karfafa hadin gwiwa a tsakaninsu.

A cewar Micheal Baafi, tun bayan da yankin ciniki mara shinge na Afrika (AfCFTA) ya fara aiki a shekarar 2019, Afrika ta zama wata babbar kasuwa ga masu zuba jari na kasar Sin. Yana mai cewa idan ana son karawa nahiyar kuzari, to kamata ya yi a samu sansanin sarrafa kayayyaki karkashin yankin.

LABARAI MASU NASABA

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

Ya kara da cewa, ya yi ammana Sinawa da mutanen Ghana za su iya hada gwiwa wajen bunkasa masana’antu a kasashen Afrika da dama.

Ya kuma bukaci kamfanonin kasar Sin su zuba jari a masana’antar samar da motoci na Afrika, inda kuma ya yi kira ga kamfanonin Ghana, su yi amfani da baje kolin wajen kulla hadin gwiwa da takwarorinsu na kasar Sin. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya
Daga Birnin Sin

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou
Daga Birnin Sin

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Next Post
Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Bayar Da Belin Dakta Idris Abdul’aziz Bisa Sharadi Uku

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Bayar Da Belin Dakta Idris Abdul'aziz Bisa Sharadi Uku

LABARAI MASU NASABA

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.