Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Hajj 2017: Mahajjatan Kebbi 553 Sawun Farko Sun Tashi

by Tayo Adelaja
August 14, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga: Umar Faruk, Birnin-kebbi

Maimartaba Sarkin Zuru Manjo Janar Mairitaya, Sani Sami  Gomo na biyu,  kuma amirul Hajji na jihar kebbi na bana, ya gabatar da jawabin bankwana da gargadi ga mahajjatan aikin hajji sawun farko 553 na jihar  kebbi, da zasu gudanar da aikin Hajji na 2017 a kasar saudi Arebiya, domin su kasance jakadun jihar kebbi da kuma kasar Nijeriya don kauce  wa ayyukan da zai iya jawo musu matsalar  ga kansu a  lokacin   da suke ƙasar mai tsarki.

samndaads

Sarkin na Zuru,  ya yi  gargadin ne a  filin jirgin sama na kasa da kasa na Sir Ahmadu Bello  da ke Birnin Kebbi yayin gabatar da jawabinsa na ban kwana ga mahajjata da suka  tashi   zuwa madina dake kasar Saudiyya a ranar assabar da misalin karfe 10:45 na dare a  matsayin sa na amirul hajji na jihar kebbi na bana.

Har ila yau,  ya hori mahajjata su kasance masu da’a  da ladabi da biyaya ga dokokin kasar saudiya a lokacin da su ke kasar.

Bugu da kari   basaraken  ya  shawarce su da cewa  aikin hajji  aiki ne wanda  ake sadaukar da kai wurin yin sa. Domin aikin hajji yana daya daga cikin shikashikan musulunci guda biyar, saboda haka duk wanda  Allah  yaba iko to ya yi kokari ya gudanar da aikin yadda ya kamata.

Hakazalika  ya  roki   mahajjata da su gudanar da addu’a ga jihar kebbi, kasar Nijeriya da kuma   Shugaba Muhammadu Buhari  da kuma  zaman lafiya da kwanciyar hankali da  hadin kai ga mutanen  kasar Nijeriya.

Mahajjata da suka  tafi sawun farko daga jihar kebbi sun fito ne  daga kananan hukumomin  Fakai, Danko-Wasagu, Bunza, Yauri ta Arewa inda suka  tashi  a filin jirgin sama na Ahmadu Bello da ke Birnin-kebbi  malakar Gwamnatin jihar ta kebbi  zuwa Madina  kasar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin bana. Wadanda kanfanin jiragen Mad Airline ya dauka.

 

Daga sarkin Zuru Sani Sami, ya yi wa mahajjatan fatar alhairi da kuma yin aikin hajji madabuliya a kuma je lafiya a dawo lafiya.

SendShareTweetShare
Previous Post

An Tsige Kakakin Majalisar Jihar Edo

Next Post

Mun Fara Binciken Jami’o’i Masu Zaman Kansu- EFCC

RelatedPosts

Misali Daga Kebbi: Yadda Kananan Hukumomi Suka Shiga Uku A Nijeriya

Misali Daga Kebbi: Yadda Kananan Hukumomi Suka Shiga Uku A Nijeriya

by Sulaiman Ibrahim
2 hours ago
0

Kamar dai yadda aka sani kananan hukumomi sune suka kasance...

Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Canja Shugabannin Tsaron Nijeriya

’Yan Yankin Arewa Maso Gabas Sun Bayyana Ra’ayoyinsu Kan Sauke Shugabannin Tsaro

by Sulaiman Ibrahim
2 hours ago
0

Biyo bayan sauke shugabannin tsaron Nijeriya tare da nada sababbi...

Ya Kashe Mata Da Yaro Da Shebur

by Sulaiman Ibrahim
2 hours ago
0

A yau aka kama wani mutum mai shekaru 28, Chukwuemeka...

Next Post

Mun Fara Binciken Jami’o’i Masu Zaman Kansu- EFCC

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version