• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Gwamnati Ta Muhimmanta Jin Dadin ‘Yan Nijeriya

by Sulaiman
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga yawancin ‘yan Nijeriya wannan ba lokaci ne na walwala a harkokin yau da kullum ba, don kuwa kusan dukkan harkokin yau da kullum na al’umma sai tashi yake yi a kullum garin Allah ya waye lamarin yana kokarin kaiwa matakin bantsoro.

Kuma babu wani fatan za a warware matsalar a nan kusa, babban abin da ke a gaban mahukunta a halin yanzu shi ne na yadda za su cigaba da rike madafun ikon tafiyar da kasa a zaben shekarar 2023, a kan haka mutum zai iya cewa, babu wani nau’i na alamun tafiyar da mulki a kasar nan a gaban su gaba daya.

  • Harin Kuje Da Tawagar Buhari: Ya Kamata A Sauya Shugabannin Tsaro – Alhaji Ibrahim

Ra’ayin wannan jaridar shi ne, a halin yanzu yakamata dukkan matakan gwamnati su dawo da akalar su a kan harkokin da suka shafi a’umma don kuwa wannan shi ne nauyi na farko da suka daukar wa kansu kuma shi ne yafi muhimmanci a kan dukkan alkawurran da suka yi a yayin da suke yakin neman zabe da kuma rantsuwar kama aiki da suka yi tun da farko.

Muna jawo hankalin masu tafiyar da gwamnati a dukkan matakai na rashin dacewar yadda aka mayar da al’umma baya, sun zama wasu da basu da wata fata na cimma wani muhimmin abu a raywarsu.

Yana da matukar sauki ‘yan Nijeriya su fahimci cewa, matsalolin da ake fuskanta a sassan kasar musamman abin da ya shafi tafiyar da rayuwa suna kara karuwa ne a kullum kuma babu wata rana da ake tunanin kawo karshen su.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Tun daga darajar Naira zuwa yadda wutar lantarki ta tabarbare da kuma yadda ake samun hauhawar farashin kayyakikn abnici, abin takaicin kuma shi ne ko a jikin ‘yan siyasar mu, duk kuwa da muna cikin kakar zabe inda yakamata a rinka tattauna irin wadannan matsaloli tare da bayanin yadda za su magance su. Ba abin da ya shafe su don kuwa a wannan zamanin sayen kuri’a ake yi ba maganar abin da aka kuduri yi wa al’umma ba.

Wannan jaridar ta lura da cewa, lallai kafin a gudanar da tarukan siyasa tare da zabar ‘yan takara a manyan jam’iyyunmu darajar Naira ta fadi warwars amma lamarin ya kara tabarbarewa ne a lokacin da aka shiga harkokin siyasar gadangadan saboda yadda aka rika kasha wa wakilai masu zabe (Deliget) kudadden kasashe wajen don sayen kuri’arsu.

‘Yan Nijeriya na kallo Naira ya ta faduwa irin faduwar da ba a taba gani ba a ‘yan shekarun nan, wanda hakan kuma ya shafi harkokin saye sayarwa a cikkin al’umma.

A ra’ayinmu babu wata bangare na tattalin arzikin kasar nan daya fi fuskantar matsalar kamar bangaren wutar lantarki.

A tsawon watanni ke nan farashin iskar gas, dizel da man fetur suka yi tashin gwauron zabi, layuka sun kara bayyana a gidajen mai kuma babu wanda zai fada maka ranar da ake ganin za a kawo karshen lamarin.

Lamarin ya kara tabarbarewa ne ta yadda aka samu labarin matsalar da ta fadawa bangaren samar da wutar lantarki inda (National grid) ya rushe.

Wadanna matsalolin sun kuma kara tayar da hankali ne ganin yadda farashin kayyakin abinci suka cigaba da ta’azzara kusan suna neman fin karfin masu karamin karfi, a halihn yanzu koda fiya wata yana neman zama wata alfarma ga ‘yan Nijeriya.

Matsalar tsaron da ake fuskanta a sasan kasar nan ya kara canza tsananin rikicin da ake fuskanta, mun yi magana sau da dama a kan wannan bangaren kuma bai kamata mu sake makalewa wajen tattauna wannan ba.

Wasu na bayar da uzurin cewa, gwamnatin nan na bayar da muhimmanci ga samar da hanyoyi da wasu aikace-aikace na raya kasa, amma a nan muna masu cewa, tabbass rayuwar al’umma yafi wani gyaran titi da za a yi, ina amfanin badi ba rai?, yakamata a bayar da karfi wajen bunkasa rayuwar al’umma.

A yanayin da manyan makarantunmu ke kulle, asibitoci suka zama kufai, kashe-kashe ya zama ruwan dare, sai a fara tunanin ko gwamnnti bata san abin daya kamata ta muhimmantar ba kenan.

Muna kira ga gwamnati a dukkan matakai su dauki abubuwan da suka shafi rayuwar al’umma da muhimmanci, Allah ya taimake mu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sallah: Gwamnan Gombe Ya Gwangwaje Mata Da Matasa Da Naira Miliyan 114

Next Post

Hajjin Bana: Alhazan Nijeriya 42,000 Da Sauran Alhazai Ne Suka Yi Tattaki Zuwa Dutsen Arafat

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 month ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Hajjin Bana: Alhazan Nijeriya 42,000 Da Sauran Alhazai Ne Suka Yi Tattaki Zuwa Dutsen Arafat

Hajjin Bana: Alhazan Nijeriya 42,000 Da Sauran Alhazai Ne Suka Yi Tattaki Zuwa Dutsen Arafat

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.