• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata

by Yusuf Shuaibu
2 months ago
in Addini
0
Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahotanni sun bayyana cewa kowanni mahajjaci daga cikin su 3,345 ya samu Riyal 50 na Saudi a matsayin tallafi a lokacin bukukuwan Sallah da kuma saukaka musa lokacin zaman su a kasar mai tsarki.

Wannan bayanin ya fito ne daga bakin wakilin Gwamna Abba Kabir Yusuf, wanda shi ne shugaban kwamitin wakilin na mahajjatan Jihar Kano, Sarkin Karaye, Alhaji Muhammad Maharaz Karaye.

  • Duk Da Jihohin Nijeriya Sun Fara Biyan Mafi Ƙarancin Albashi Na 70,000, Ana Ci Gaba Da Fuskantar Matsin Rayuwa
  • Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka

Sarkin ya isar da sakon gwamnan a yayin da yake yi wa mahajjatan Jihar Kano jawabi a gidan Shari Mansur a Makkah, sarkin ya isar da sakon Gwamna Yusuf.

Sakataren Kwamitin kuma Daraktan Janar na Hukumar Kula da Jin Dadin Alhazai ta a Jihar Kano, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa, ya ce tsarin rarraba kudin ya gudana cikin cikakken tsari.

Ya kuma ce ya sanar da karin tanadi ga mahajjatan, wanda zai ga kowannensu ya karbi babban akwati na tafiya a shirin dawowarsu gida.

Labarai Masu Nasaba

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (1)

Babban Al’amari Ne A Samu Ƴar Shekara 6 Ta Haddace Qur’ani A Makarantar Raudatul Jannah – Mai Sikeli

Haka zalika, Gwamnatin Jihar Kebbi ba ta bayar da tallafi ga mahajjantanta 3,800 daga jihar ba. Amma a kasar Saudiyya, Gwamnan Nasir Idris ya amince da bayar da Riyal 200 ga kowane alhaji daga jihar.

Gwamnatin Jihar Lagos ba ta tallafi ga mahajjatanta a wannan shekara ba, yayin da kowane daga cikin masu aikin hajji 1,315 daga jihar ya biya kimanin naira miliyan 9.

Amma kuma, Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya ba kowane daga cikin mahajjatan kyauta Riyal 180, wanda ya kai naira 98,454,050 gaba dayansu.

Gwamnatin Jihar Jigawa, wacce ma ba ta bayar da tallafi ga mahajjatanta ba a wannan shekarar, amma ta ba su kyautar Riyal 100 (kimanin naira 43,000) ga kowanne daga cikin mahajjatanta 930.

Dukkanin alhazai Jihar Sakkwato 3,200 sun karbi Riyal 1,000 (wanda ya kai kimanin naira 450,000) a matsayin kyautar sallah daga Gwamna Ahmed Aliyu.

Gwamnan ya sanar da hakan a ranar Asabar yayin ziyararsa ga tawagar alhazan jihar a Mina da ke kasar Saudiyya, inda ya taya su murnar kammala aikin hajj cikin nasara.

Mataimakin gwamnan Jihar Borno, Umar Usman Kadafur, ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta biya kudin hadiyya ga kowane alhazi daga jihar. Adadin alhazan sun kai 2,174, da suka yi aikin hajji a wannan shekara daga jihar.

Wani masani kan harkokin al’umma, Farfesa Yahaya Tanko, a cikin wata hirar, ya bayyana cewa kashe kudin da gwamnonin suka yi kan aikin hajji ba matsala ba ce, amma sun manta da asalin abin da al’ummarsu suka fi bukata.

Ya ce ya kamata gwamnonin su fi mai da hankali kan magance matsalar tsaro da inganta jin dadin ‘yan kasa.

Da yake jawabi kan lamarin, babban limanin Al-Habibiyah Islamic Society (AIS), Sheikh Fuad Adeyemi, ya ce ba laifi ba ne ga gwamnatin tarayya da na jihohi su tallafa wa masu alhazai, amma ya kamata a yi amfani da kudaden wajen abubuwan da mutane suka fi bukata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hajji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wanda Ya Yi Gangancin Taba Takarar Shettima Ya Gayyato Wa APC Faɗuwa A 2027 – Aminu Boyi 

Next Post

Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani – Daurawa

Related

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (1)
Addini

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (1)

2 months ago
Babban Al’amari Ne A Samu Ƴar Shekara 6 Ta Haddace Qur’ani A Makarantar Raudatul Jannah – Mai Sikeli
Addini

Babban Al’amari Ne A Samu Ƴar Shekara 6 Ta Haddace Qur’ani A Makarantar Raudatul Jannah – Mai Sikeli

2 months ago
Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani – Daurawa
Addini

Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani – Daurawa

2 months ago
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
Manyan Labarai

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

3 months ago
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)
Addini

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)

3 months ago
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci
Addini

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

4 months ago
Next Post
Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani – Daurawa

Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur'ani - Daurawa

LABARAI MASU NASABA

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.