• English
  • Business News
Saturday, June 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata

by Yusuf Shuaibu
2 hours ago
in Addini
0
Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahotanni sun bayyana cewa kowanni mahajjaci daga cikin su 3,345 ya samu Riyal 50 na Saudi a matsayin tallafi a lokacin bukukuwan Sallah da kuma saukaka musa lokacin zaman su a kasar mai tsarki.

Wannan bayanin ya fito ne daga bakin wakilin Gwamna Abba Kabir Yusuf, wanda shi ne shugaban kwamitin wakilin na mahajjatan Jihar Kano, Sarkin Karaye, Alhaji Muhammad Maharaz Karaye.

  • Duk Da Jihohin Nijeriya Sun Fara Biyan Mafi Ƙarancin Albashi Na 70,000, Ana Ci Gaba Da Fuskantar Matsin Rayuwa
  • Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka

Sarkin ya isar da sakon gwamnan a yayin da yake yi wa mahajjatan Jihar Kano jawabi a gidan Shari Mansur a Makkah, sarkin ya isar da sakon Gwamna Yusuf.

Sakataren Kwamitin kuma Daraktan Janar na Hukumar Kula da Jin Dadin Alhazai ta a Jihar Kano, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa, ya ce tsarin rarraba kudin ya gudana cikin cikakken tsari.

Ya kuma ce ya sanar da karin tanadi ga mahajjatan, wanda zai ga kowannensu ya karbi babban akwati na tafiya a shirin dawowarsu gida.

Labarai Masu Nasaba

Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata AlÆ™ur’ani – Daurawa

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Haka zalika, Gwamnatin Jihar Kebbi ba ta bayar da tallafi ga mahajjantanta 3,800 daga jihar ba. Amma a kasar Saudiyya, Gwamnan Nasir Idris ya amince da bayar da Riyal 200 ga kowane alhaji daga jihar.

Gwamnatin Jihar Lagos ba ta tallafi ga mahajjatanta a wannan shekara ba, yayin da kowane daga cikin masu aikin hajji 1,315 daga jihar ya biya kimanin naira miliyan 9.

Amma kuma, Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya ba kowane daga cikin mahajjatan kyauta Riyal 180, wanda ya kai naira 98,454,050 gaba dayansu.

Gwamnatin Jihar Jigawa, wacce ma ba ta bayar da tallafi ga mahajjatanta ba a wannan shekarar, amma ta ba su kyautar Riyal 100 (kimanin naira 43,000) ga kowanne daga cikin mahajjatanta 930.

Dukkanin alhazai Jihar Sakkwato 3,200 sun karbi Riyal 1,000 (wanda ya kai kimanin naira 450,000) a matsayin kyautar sallah daga Gwamna Ahmed Aliyu.

Gwamnan ya sanar da hakan a ranar Asabar yayin ziyararsa ga tawagar alhazan jihar a Mina da ke kasar Saudiyya, inda ya taya su murnar kammala aikin hajj cikin nasara.

Mataimakin gwamnan Jihar Borno, Umar Usman Kadafur, ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta biya kudin hadiyya ga kowane alhazi daga jihar. Adadin alhazan sun kai 2,174, da suka yi aikin hajji a wannan shekara daga jihar.

Wani masani kan harkokin al’umma, Farfesa Yahaya Tanko, a cikin wata hirar, ya bayyana cewa kashe kudin da gwamnonin suka yi kan aikin hajji ba matsala ba ce, amma sun manta da asalin abin da al’ummarsu suka fi bukata.

Ya ce ya kamata gwamnonin su fi mai da hankali kan magance matsalar tsaro da inganta jin dadin ‘yan kasa.

Da yake jawabi kan lamarin, babban limanin Al-Habibiyah Islamic Society (AIS), Sheikh Fuad Adeyemi, ya ce ba laifi ba ne ga gwamnatin tarayya da na jihohi su tallafa wa masu alhazai, amma ya kamata a yi amfani da kudaden wajen abubuwan da mutane suka fi bukata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hajji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wanda Ya Yi Gangancin Taba Takarar Shettima Ya Gayyato Wa APC FaÉ—uwa A 2027 – Aminu Boyi 

Next Post

Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata AlÆ™ur’ani – Daurawa

Related

Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata AlÆ™ur’ani – Daurawa
Addini

Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata AlÆ™ur’ani – Daurawa

1 hour ago
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
Manyan Labarai

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

2 weeks ago
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)
Addini

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)

3 weeks ago
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci
Addini

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

1 month ago
An Gano Cushen Biliyan 5 Cikin Kasafin Kuɗin Hukumar Alhazai Ta Ƙasa
Addini

An Gano Cushen Biliyan 5 Cikin Kasafin Kuɗin Hukumar Alhazai Ta Ƙasa

1 month ago
Nijeriya Za Ta KarÉ“i Bakuncin Gasar Karatun AlÆ™ur’ani Mai Girma Ta Duniya
Addini

Nijeriya Za Ta KarÉ“i Bakuncin Gasar Karatun AlÆ™ur’ani Mai Girma Ta Duniya

2 months ago
Next Post
Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata AlÆ™ur’ani – Daurawa

Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur'ani - Daurawa

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Gargaɗi Masu Lalata Fastar Tinubu A Kano

Ƴansanda Sun Gargaɗi Masu Lalata Fastar Tinubu A Kano

June 21, 2025
Minista Ya Yaba Wa Hafsoshin Soji Kan Cigaban Da Aka Samu A Fannin Tsaron Ƙasa

Minista Ya Yaba Wa Hafsoshin Soji Kan Cigaban Da Aka Samu A Fannin Tsaron Ƙasa

June 21, 2025
Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata AlÆ™ur’ani – Daurawa

Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata AlÆ™ur’ani – Daurawa

June 21, 2025
Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata

Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata

June 21, 2025
Wanda Ya Yi Gangancin Taba Takarar Shettima Ya Gayyato Wa APC FaÉ—uwa A 2027 – Aminu Boyi 

Wanda Ya Yi Gangancin Taba Takarar Shettima Ya Gayyato Wa APC FaÉ—uwa A 2027 – Aminu Boyi 

June 21, 2025
Iran Ta Bayyana SharaÉ—in Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje

Iran Ta Bayyana SharaÉ—in Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje

June 21, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Duk Da Jihohin Nijeriya Sun Fara Biyan Mafi Ƙarancin Albashi Na 70,000, Ana Ci Gaba Da Fuskantar Matsin Rayuwa

June 21, 2025
Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 

Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 

June 20, 2025
Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka

Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka

June 20, 2025
Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?

Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?

June 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.